Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta
Published: 8th, June 2025 GMT
Ministan Bunƙasa Harkokin Ƙarafa, Shuaibu Abubakar Audu, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na samun ci gaba wajen farfaɗo da tsohon kamfanin ƙarafa na Ajaokuta da ke Jihar Kogi.
Ya bayyana hakan ne a wani taro da ya gudanar da manyan jiga-jigan jam’iyyar APC na Jihar Kogi a garinsu Ogbonicha da ke Ƙaramar Hukumar Ofu.
Ministan, ya ce Gwamnatin Tarayya ta riga ta rattaba hannu kan yarjejeniya da kamfanonin da za su samar da kayan aikinkamfanin.
Ya ƙara da cewa gwamnati na ƙara neman masu saka hannun jari daga ƙasar China domin su zuba jari a kamfanin.
“Muna yin aiki babba. Mun fara tafiya, kuma muna da tabbacin cewa za mu dawo da aikin Ajaokuta cikin sauri,” in ji Audu.
Ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu saboda tsare-tsarensa na gyara da ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar nan ta hanyar inganta harkar sarrafa ƙarafa.
Ya ce Shugaban Ƙasa na ƙoƙarin warware matsalolin da ke addabar ƙasar nan da kuma inganta rayuwar ‘yan ƙasa.
Audu, ya ce shirin “Sabunta Fata” da Shugaban Ƙasa ke jagoranta ya riga ya fara haifar da ɗa mai ido.
Ya bayyana saukar farashin wasu kayan abinci a matsayin misali.
Haka kuma ya bayyana cewa kuɗin da jihohi ke samu daga Asusun Gwamnatin Tarayya (FAAC) sun ƙaru, lamarin da ya taimaka wa Jihar Kogi.
A nasa jawabin, Sakataren APC na Jihar Kogi, Joshua Onoja, ya yaba wa Ministan bisa shirya taron, sannan ya tabbatar da cikakken goyon bayan jam’iyyar wajen sake zaɓen Shugaba Tinubu a 2027.
Taron ya samu halartar shugabannin jam’iyyar daga sassa daban-daban na Jihar Kogi, ciki har da shugabannin ƙananan hukumomi, ’yan majalisa na yanzu da na baya, ƙungioyi da sauransu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Kamfanin Ƙarafa Gwamnatin Tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na Naira Biliyan 75 na shekarar 2025, ga gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi 27.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan zaman majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa, wannan ƙarin kasafin kuɗi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga domin biyan buƙatun kuɗaɗen da suka taso, da kuma ƙarfafa manyan fannoni da za su kawo ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, majalisar ta amince da Naira Biliyan 58 ga gwamnatin jiha da kuma Naira Biliyan 17 ga Kananan Hukumomi 27, wanda ya shafi kashe-kashen kudade na yau da kullum da kuma manyan ayyuka.
Ya ce, wannan ƙarin kasafin kuɗin zai inganta ayyuka da tsare-tsare da ake gudanarwa a muhimman fannoni irin su ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, noma da sauran muhimman ayyukan ci gaba.
Sagir ya ƙara da cewa, za a mika ƙarin kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Jihar domin tattaunawa da amincewa da shi, kamar yadda kundin tsarin mulki da ka’idojin kasafi suka tanada.
Kwamishinan ya ƙara jaddada cewa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci, da kula da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace, da kuma tabbatar da samar da ingantattun ayyuka ga al’ummar jihar baki ɗaya.
Usman Muhammad Zaria