Aminiya:
2025-06-22@18:12:26 GMT

Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta

Published: 8th, June 2025 GMT

Ministan Bunƙasa Harkokin Ƙarafa, Shuaibu Abubakar Audu, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na samun ci gaba wajen farfaɗo da tsohon kamfanin ƙarafa na Ajaokuta da ke Jihar Kogi.

Ya bayyana hakan ne a wani taro da ya gudanar da manyan jiga-jigan jam’iyyar APC na Jihar Kogi a garinsu Ogbonicha da ke Ƙaramar Hukumar Ofu.

Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da duka

Ministan, ya ce Gwamnatin Tarayya ta riga ta rattaba hannu kan yarjejeniya da kamfanonin da za su samar da kayan aikinkamfanin.

Ya ƙara da cewa gwamnati na ƙara neman masu saka hannun jari daga ƙasar China domin su zuba jari a kamfanin.

“Muna yin aiki babba. Mun fara tafiya, kuma muna da tabbacin cewa za mu dawo da aikin Ajaokuta cikin sauri,” in ji Audu.

Ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu saboda tsare-tsarensa na gyara da ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar nan ta hanyar inganta harkar sarrafa ƙarafa.

Ya ce Shugaban Ƙasa na ƙoƙarin warware matsalolin da ke addabar ƙasar nan da kuma inganta rayuwar ‘yan ƙasa.

Audu, ya ce shirin “Sabunta Fata” da Shugaban Ƙasa ke jagoranta ya riga ya fara haifar da ɗa mai ido.

Ya bayyana saukar farashin wasu kayan abinci a matsayin misali.

Haka kuma ya bayyana cewa kuɗin da jihohi ke samu daga Asusun Gwamnatin Tarayya (FAAC) sun ƙaru, lamarin da ya taimaka wa Jihar Kogi.

A nasa jawabin, Sakataren APC na Jihar Kogi, Joshua Onoja, ya yaba wa Ministan bisa shirya taron, sannan ya tabbatar da cikakken goyon bayan jam’iyyar wajen sake zaɓen Shugaba Tinubu a 2027.

Taron ya samu halartar shugabannin jam’iyyar daga sassa daban-daban na Jihar Kogi, ciki har da shugabannin ƙananan hukumomi, ’yan majalisa na yanzu da na baya, ƙungioyi da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Kamfanin Ƙarafa Gwamnatin Tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya

Jagororin jam’iyyun adawa na Najeriya a ƙarƙashin ƙungiyar hadaƙa ta Nigeria National Coalition Group (NNCG) na neman yin rajistar All Democratic Alliance (ADA) domin ta zama sabuwar jam’iyyar da za su yi amfani da ita don tunkarar  Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

NNCG ta riga ta miƙa takardar neman rajistar jam’iyya ga Hukumar Zaɓe mai zaman kanta INEC a hukumance don babban zaɓe na gaba.

Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom

Takardar wadda suka aika zuwa ga shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu a ranar 19 ga watan Yuni, wanda shugaban ADA na ƙasa Cif Akin Ricketts da sakataren riƙo Abdullahi Musa Elayo ne suka sanya mata hannu, sannan INEC ta karɓa tare a ranar Juma’a 20 ga Yunin.

A takardar an rubuta cewa, “muna neman INEC ta amince da buƙatarmu ta yi wa ƙungiyarmu ta All Democratic Alliance (ADA) ta zama jam’iyyar siyasa.”

Ta ƙara da cewa, taken jam’iyyar dai shi ne ‘Adalci ga kowa’ sannan masara ce tambarinta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
  • 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya