Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza
Published: 10th, June 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya zanta ta wayar tarho da firay ministan HKI Benyamin Natanyahu kan kasar Iran da kuma yakin Gaza.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa majiyar ofishin Natanyahu ta bayyana cewa tattaunawar tana zuwa ne a dai-dai lokacinda rikici da yaki yake ci gaba a gaza, da kuma tattaunawa kan shirin Nuclear kasar Iran ke ci gaba.
Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Amurka na jirin jawabin da kasar Iran zata mayar masa dangane da shawarar da ya gabatar na warware matsalar tashe makamancin Yuranium a Iran.
Har’ila yau ya na jiran jawabin da kungiyar Hamas za ta bayar kan yarjeniyar dakatar da yaki a Gaza.
Shugaban dai yana cikin matsin lamba don ganin an warware wadannan al-amura guda biyu na gabas ta tsakiya.
Tattaunawar wanda bai fi mintoci 40 ba, ya bukaci gwamnatin Natanyaho ta shirya daukar matakan gaggawa bayan da shugaban ya sami wadannan sakonnin da yake jira.
Don haka ne ake saran Natanyanhu zai gudanar da taron gaggawa tare da manya manyan jami’an gwamnatinsa a ma’aikatar tsaro ko yakin na kasar, don tattauna wadannan al-amura.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
Gwamnatin kasar Spaine ta soke kontaragin sayan makama daga HKI wadanda yawansu ya kai Euro Miliyon 700, saboda kissan kiyashin da ke faruwa a gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a jiya Litinin ne gwamnatin firay minister Pedro Sanchez ta bada wannan sanarwan ta kuma kara da cewa makaman su ne makamai masucilla rokoki samfurin Elbit kirar HKI.
Labarin ya kara da cewa Madrid ta soke wani kontaragi wanda ya kai Eur miliyon 287 da HKI. Na sayan garkuwan tankunan yaki wadanda za’a kerasu a kasar karkashin lacicin HKI a kasar Espania.
Banda haka firay minister Pedro Sanchez ya bukaci a haramta HKI daga dukkanin wasannin nakasa da kasa saboda kissan kiyashin da take aikata a gaza a ranar Lahadin da ta gabata.
Gwamnatin kasar ta Espania tabayyana cewa tanada shirin daukar wasu karin matakan kan HKI saboda kissan kiyashin datake aikatawa Gaza.
Daga cikinsu har da haramtawa dukkan yahudawan da suke da hannu cikin kissan kiyashin shiga kasar Espania .
Sannan akwai takunkuman tattalin arzikin na hana sayan dukkan kayakin da ake kerawa a kasar Falasdinu da aka mamaye.
Daga karshen gwamnatin kasar Espania ta zargi kasashen turai kan nuna fuska biyu a kissan kiyashin Gaza, idan an kwatanta da na Ukraine.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci