Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya zanta ta wayar tarho da firay ministan HKI Benyamin Natanyahu kan kasar Iran da kuma yakin Gaza.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa majiyar ofishin Natanyahu ta bayyana cewa tattaunawar tana zuwa ne a dai-dai lokacinda rikici da yaki yake ci gaba a gaza, da kuma tattaunawa kan shirin Nuclear kasar Iran ke ci gaba.

Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Amurka na jirin jawabin da kasar Iran zata mayar masa dangane da shawarar da ya gabatar na warware matsalar tashe makamancin Yuranium a Iran.

Har’ila yau ya na jiran jawabin da kungiyar Hamas za ta bayar kan yarjeniyar  dakatar da yaki a Gaza.

Shugaban dai yana cikin matsin lamba don ganin an warware wadannan al-amura guda biyu na gabas ta tsakiya.

Tattaunawar wanda bai fi mintoci 40 ba, ya bukaci gwamnatin Natanyaho ta shirya daukar matakan gaggawa bayan da shugaban ya sami wadannan sakonnin da yake jira.

Don haka ne ake saran Natanyanhu zai gudanar da taron gaggawa tare da manya manyan jami’an gwamnatinsa a ma’aikatar tsaro ko yakin na kasar, don tattauna wadannan al-amura.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta ce a shirye take ta shiga tsakani a kokarin samar da zaman lafiya tsakanin Pakistan da Indiya

Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian ya bayyana shirin kasarsa na samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin kasaahen Pakistan da Indiya.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif a ranar Asabar.

Shugaban na Iran ya ce manufar Iran ta mayar da hankali ne kan inganta samar da zaman lafiya a duniya musamman a cikin kasashen musulmi.

Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci tana maraba da duk wani mataki da kokarin samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin Pakistan da Indiya, kuma za ta iya taka rawar shiga tsakani ga wannan manufar.”

A nasa bangaren firaministan kasar Pakistan ya mika sakon gaisuwar babba salla da sakon fatan alheri ga al’ummar Iran da kuma jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Sharif ya kuma bayyana fatan ganin an aiwatar da yarjejeniyoyin kasashen biyu da Pakistan da Iran suka kulla.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  
  • Za’ayi tattaunawa ta gaba tsakanin Iran da Amurka a ranar Lahadi a Oman
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Tace Sinadarin Uranium
  • Jami’in Makamashin Nukiyar Iran Ya Ce; Zarge-Zargen Da Ake Yi Kan Shirin Makmashin Nukiliyar Iran Siyasa Ce Kawai
  • Iran Tace Amurka Tana Ci Gaba Da Amfani Da Karfi Inda Bai Dace Ba A Duniya
  • Iran ta ce a shirye take ta shiga tsakani a kokarin samar da zaman lafiya tsakanin Pakistan da Indiya
  • Iran Ta Sami Muhimman Bayanai Na Sirri Akan Shirin Nukiliyar HKI
  • Iran A Shirye Take Ta Bada Dama A Gudanar Da Bincike A Cibiyoyin Nukliyar Kasar
  • Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran