HausaTv:
2025-06-11@01:13:39 GMT

Iran Ta Ce Wuraren Kai Farmaki A HKI Suna Hannu a Duka Sanda Ta Kawo hari Iran

Published: 10th, June 2025 GMT

Majalisar koli ta tsaron kasar Iran ta bayyana cewa jerin wuraren da zata kaiwa hare hare a HKI a duk wani yakin da zata taso tsakanin kasshen biyu, suna hannu. Daga ciki har da ciboyoyin Nukliyar kasar wadanda ta boye su.

Tashar talabjin ta Presstv a nann Tehran ta nakalto majalisar ta na fadar haka a jiya Litinin, ta kuma kara da cewa ta kara samun bayanai masu muhimmanci a wannan fagen, bayan bayanan leken asirin da ta samu a cikin yan kwanakin da sukka gabata.

Labarin ya kara da cewa a halin yanzu sojojin JMI suna cikin shiri fiye da na ko wani lokaci, don maida martani ga makiya.

Tace a halin yanzu jerin wuraren da sojojin Iran zasu kaiwa hare-hare a HKI, hatta kan wurarenda wadanda HKI ta boye su, suna hannu, kuma zata sha mamaki idan ta kuskura ta takali Iran da yaki.

Dangane da dimbin bayanan sirri da kasar ta samu kuma, majaliasar ta kara karfafa shirin kare kasar daga HKI saboda samunsu.

Har’ila yau suna da cikakkun bayanan wuraren da zasu kaiwa hari, gwagwadon wauraren da HKI ta taba a cikin kasar Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Hare Kan Birnin Hudaida Na Kasar Yemen A Safiyar Yau Talata

Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan birnin Hudaidah na bakin ruwa a kasar Yemen a safiyar yau Talata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto tashoshin talabijin ta Almasirahtv ta kasar Yemen, da kuma Aljazeerah ta kasar Qatar  suna bada wannan labarin.

Sun kuma kara da cewa tun fara yaki a Gaza a shekara ta 2023 sojojin kasar Yemen suka hana jiragen kasuwanci na HKI wucewa ta babul Mandab na kasar Yemen wanda ya jawowa HKI asarori masu yawa, ya kuma gurgurta ayyukan tashoshin jiragen Ruwa na ummu Rashrash ko Ilat da kuma Haifa.

Sannan suna kaiwa hki hare-hare ne da makamai masu linzami kan tashar jiragen sama na Bengerion da kuma wuraren soje na kasar tun lokacin

Yemen na yin haka ne don goyon bayan  ga al-ummar Falasdinawa wadanda sojojin HKI suke ci gaba da yi masu kisan kare dangi tun lokaci har zuwa yanzu. Falasdinawa kimani 54000 hki ta kace ya zuwa yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza 
  • Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Hare Kan Birnin Hudaida Na Kasar Yemen A Safiyar Yau Talata
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Fara Sana’a Ba Tare Da Jari Ba
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayanan Tsaron HKI
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI
  • Iran Ta Sami Muhimman Bayanai Na Sirri Akan Shirin Nukiliyar HKI
  • Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran