HausaTv:
2025-07-23@23:42:43 GMT

HKI Ta Kashe Wani Babban A Cikin Shuwagabannin Falasdinawa

Published: 8th, June 2025 GMT

Daya daga cikin shuwagabannin Falasdinawa ya yi shahada sanadiyyar hare-haren da sojojin HKI suka kai kan zirin gaza.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Asa’d Abu Sharia shi ne baban sakataren kungiyar ‘Dakarun Palastinewa”. Wacce aka kafa a shekara ta 2001 M.

Kungiyar kanta ta tabbatar da wannan labarin ta kuma bayyana cewa ya dade yana shugabantar wannan kungiyar sannan a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ya shiga cikin yakin da aka fara kan HKI kuma dakarunsa sun kama yahudawa da dama suka shigo da su su gaza.

Banda haka shi ne yake jagorantar bangaren soje na kungiyarsa. Sau da dama ya jagoranci Falasdinawa a yaki da yahudawan a Gaza. Sannan kungiyar tana da reshe a yankin yamma da kogin Jordan.

A wani labarin kuma kungiyar ta kara da cewa tare da shi akwai dan uwansa Ahmed Abu Sharia, ko wanda akewa  Lakabi da  Abu Falasteen, sun yi shahada tare. Banda haka kafin shahadarsa Abu Sharia ya rasa danginsa na kusa kimani 150 a yankin tufanul Aksa ya zuwa yanzu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki

Kungiyoyin agaji da kuma na hakkokin bil’adama sun yi gargadi akan yunwar da ake fama da ita a Gaza, tare da yin kira ga gwamnatoci da su yin matsin lamba domin kawo karshe killace Gaza da aka yi, da kuma shigar da kayan agaji a cikin yanki.

Kungiyoyin sun kuma dorawa HKI alhakin halin da mutanen Gaza suke ciki na yunwa.

Daga cikin kungiyoyin da su ka fitar da bayani da akwai Majalisar ‘yan gudun hijira ta kasar Norway” da “Refugee International” da wasu da adadinsu ya kai 111, sun yi gargadi akan yadda yunwa take yaduwa a cikin Gaza.

Bayanin ya kunshi cewa; Mazauna yankin Gaza suna fama da yunwa saboda killace su da Isra’ila ta yi, kuma a duk lokacin da mutanen su ka nunfi wurin da aka ware domin raba abinci sai a bude musu wuta.

Wuararen raba abincin da suke a cikin yankin Gaza dai, HKI da Amurka su ka shriya su a matsayin tarkon kashe Falasdinawa da suke zuwa wurin.

Bayanin ya kuma ce, da akwai kayan abinci, ruwa da magunguna masu yawan gaske da aka ajiye da su a wajen yankin Gaza, amma kuma Isra’ila  ta hana a shiga da su.

Haka nan kuma sun bayyana cewa; Dukkanin kayan agajin da ake da su, sun kare baki daya, kuma kungiyoyin agaji suna Kallon yadda ‘yan’uwansu suke ramewa da kama hanyar mutuwa saboda rashin abinci.

Har ila yau sun yi ishara da cewa: Dokoki da Isra’ila ta kafa ne, da su ka jawo jinki, da kuma yadda take karkatsa yankin na Gaza wanda yake a killace, su ne su ka  haddasa yunwa da mutuwa.”

 Haka nan kuma wadannan kungiyoyin sun yi kira ga gwamnatoci da su kawo karshen bin matakai na cike-ciken takardu akan dukkanin hanyoyi, saboda share fagen shigar da kayan abinci cikin  yankin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Yahudawan Sahayoniyya Sun Bullo Da Dabarar Kisa Kan Falasdinawa Musamman ‘Yan Gudun Hijira
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi