HausaTv:
2025-07-25@00:51:12 GMT

HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai

Published: 9th, June 2025 GMT

Wadanda suka shirya jirgin agaji zuwa Gaza mai suna Madleen sun bada sanarwan cewa HKI kai farmaki kan jirgin a safiyar yau Litinin.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa jami’an tsaron HKI sun kaiwa jirgin Madleen hare-hare a safiyar yau Litinin kafin iasar Jirgin agajin zuwa gabar tekun Medeterania a gaza.

Labarin ya kara da cewa Thiago Avila, dan rajin kare hakkin bil’adama daga kasar Brazil a cikin Jirgin ya bayyana cewa sojojin yahudawan sun yiwa jirgin kofar rago  .  Y ace sojojin ruwa na HKI sun kaiwa jirgin agaji ” Madleen farmakai. Jirgi wanda yake kokarin  keta kofar ragon da HKI ta yi wa Gaza tun shekara 2006.

Labarin ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kama masu rajen kare hakkin mutanen Gaza, dake cikin jirgin ruwa na Madleen saboda an daina jinn duriyarsu.

Daga cikin wadanda suke cikin wannan jirgin dai, wadanda kuma suke tsare a hannun jami’an tsaron HKI sun hada da Greta Thunberg mai rajin kare yanayi, sannan mutane 12 wadanda suke rajin kare mutanen Gaza ta hanyar Jirgin Madleen, da kuma

Sai kuma Liam Cunningham da Rima Hassan, yan majalisar dokokin Taarayyar Turai daga kasar faransa kuma yan asalin kasar Falasdinu. Labarin yace LIMA ta yada sautin da karar jiniyar da sojojin yahudawan suka kunna a lokacin kai masu hari.

Kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya nakalto Mahmood Abu-Odeh dan jarida wanda yake bin jirin ceton na Madleen daga kasar Jamus ya bayyana cewa an kama wadanda suke jirgin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya bukaci Isra’ila ta saki wani ma’aikacin hukumar da ya ce sojojin Isra’ila sun kama a wani farmaki da suka kai a tsakiyar Gaza ranar Litinin.

Tedros Ghebreyesus ya ce sojojin sun jefa ma’aikatan agaji da iyalansu cikin hatsari a lokacin da suka shiga gidajensu da kuma babban dakin ajiyar kaya a Deir al-Balah.

Ya yi alƘawarin cewa WHO za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta a yankin.

Deir al-Balah dai na cike makil da Falasɗinawa da suka rasa matsugunansu a kusan shekaru biyu na yakin Gaza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China
  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza