Shugaban kasar Amurka ya ci gaba da fadin kalamai na zagi ga tsohon mai taimaka masa a harkokin gwamnati bayan sun babe.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Trump yana cewa hamshaken  attajirin ya haukace.

Labarin ya nakalto Fadar white house na karyata zancen cewa mutanen biyu zasu dinke barakan da ta faru a tsakaninsu wanda yasa shugaban ya kore shi.

Wani mai Magana da yawun fadar white House yana cewa shugaban bai da wani shin a Magana da Musk a yau.

Ya ce Trump ba ya kaunar sake ganinsa, duk da cewa Musk ya bayyana anniyarsa ta gyaran barakar da ta barke a tsakaninsa da maigidansa shugaba Trump.

A safiyar jiya Jumma’a Trump ya fadawa radiyon ABC kan cewa bai son ganin Musk kuma ballanta na ya zanta da shi.

Kafin haka dai Musk ya ce Trump bai da godiya, kuma ya nuna butulci ,  don ba zai lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a shekarar da ta gabata ba idan bas hi ba. Don haka shi ya sa shi a fadar white House.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya

Cibiyar Adalci, Ci gaba da Jinƙai ta mabiya ɗarikar Katolika (JDPC) reshen Kafanchan, tare da haɗin guiwar Majalisar Matan Katolika, ta shirya taron horaswa ga shugabannin addini da na gargajiya daga ƙananan hukumomin Jama’a da Zangon Kataf a Kudancin Jihar Kaduna.

Taron, wanda aka gudanar a garin Kafanchan a ƙarƙashin shirin Community Action for Peace and Socio-Economic Development (CAPSED), ya mayar da hankali ne kan zaman lafiya da kuma noma mai ɗorewa, musamman ma yadda ake amfani da takin gargajiya wajen noman citta.

Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari

Taron wanda Hukumar Agajin Katolika ta Ƙasashen Waje (CAFOD) ta ɗauki nauyi na da nufin magance abubuwan da ke haifar da rikici da kuma inganta hanyoyin noma na zamani domin samar da zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a yankin.

A cikin jawabinsa, Rabaran Dakta James Movel Wuye ya jaddada muhimmancin magance mummunan fahimta da ƙyashi tsakanin al’umma.

Ya ce, “Idan muka magance waɗannan matsalolin yadda ya kamata, za mu samu damar rage ƙiyayya da gaba tsakanin ƙabilu da addinai daban-daban a ƙasarmu.” Ya ja kunnen mahalarta game da faɗin kalaman ƙiyayya, yana mai cewa hakan na iya haifar da rikici da kuma cutar da lafiyar ƙwaƙwalwar wanda ake faɗawa hakan.

Da yake jawabi a ɓangaren noma, Dakta Barak Zebedee ya yi bayani ne kan amfani da hanyoyin fasaha wajen gudanar da noma na gargajiya musamman a ɓangaren noman citta. Ya bayyana cewa kakar noma ta shekarar 2023 ta zo da ƙalubale iri-iri na cututtukan citta inda ya shawarci manoma da su rungumi sababbin hanyoyin da ke da kariya daga cutar don samun ribar noma da ɗorewar amfanin gona.

Da yake nasa jawabin tunda farko, shugaban shirin CAPSED, Rabaran Fr. Onuh Ladi, ya bayyana cewa matakin farko na shirin ya samu gagarumin tasiri, musamman wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin mabiya addinai a cikin al’umma.

Ya ce, wannan zagaye na biyu zai ƙara jaddada batun lafiyar ƙwaƙwalwa da kuma gabatar da sabbin dabarun sasanci ba tare da zuwa kotu ba.

Ya ce, “Manufarmu ita ce, mu ba shugabanni ƙarfin gwiwa da dabarun magance rigingimu cikin gaggawa kafin lamarin ya gagari kundila. A ɓangaren noma kuma, mun ƙarfafa sauya fasalin daga amfani da sinadarai zuwa ga taki na gargajiya, musamman a noman citta,” in ji Fr. Ono.

Ya kuma bayyana cewa, mahalarta za su ci gaba da yaɗawa da koyar da abin da suka koya a cikin al’ummominsu don saƙon ya game sauran manoman da ba su samu damar halartar bitar ba.

Wasu daga cikin mahalarta da suka tattauna da wakilinmu sun nuna godiya da farin ciki da horon da suka samu, inda suka ce ya faɗaɗa fahimtarsu game da koyarwar addinin Musulunci da na Kiristanci kan zaman lafiya da haƙuri. Haka kuma, sun ce zaman ya taimaka musu wajen warware wasu tunanin ba su da tushe a cikin sahihan koyarwar addinansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho