Shugaban Trump Ya Ci Gaba Da Musayar Zage-Zage Da Aboki Da Kuma Tsohon Mai Bashi Shawara Musk
Published: 7th, June 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka ya ci gaba da fadin kalamai na zagi ga tsohon mai taimaka masa a harkokin gwamnati bayan sun babe.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Trump yana cewa hamshaken attajirin ya haukace.
Labarin ya nakalto Fadar white house na karyata zancen cewa mutanen biyu zasu dinke barakan da ta faru a tsakaninsu wanda yasa shugaban ya kore shi.
Ya ce Trump ba ya kaunar sake ganinsa, duk da cewa Musk ya bayyana anniyarsa ta gyaran barakar da ta barke a tsakaninsa da maigidansa shugaba Trump.
A safiyar jiya Jumma’a Trump ya fadawa radiyon ABC kan cewa bai son ganin Musk kuma ballanta na ya zanta da shi.
Kafin haka dai Musk ya ce Trump bai da godiya, kuma ya nuna butulci , don ba zai lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a shekarar da ta gabata ba idan bas hi ba. Don haka shi ya sa shi a fadar white House.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Farfesa Jibril Amin Tsoho Ministan Ilim Da, Manfetur A Najeriya Rasu Yana Dan Shekara 85 A Duniya
Farfesa Jibril Amin Likita kuma tsohon malamin Jami’a, ya rasu a jiya Laraba yana dan shekara 85 a duniya.
Jaridar Daily Trusta ta Najeriya ta nakalto majiyar iyalar mamacin na tabbatar da haka. Ta kuma bayyana cewa kwamishin gidaje a jihar Adama Hon Abdullahi Prambe ya tabbatar da labarin. Sannan ya kara da cewa an yi masa sallar Jana’iza a babban masallacin kasa a Abuja a yau Alhamis. Sannan za’a maida shi garinsa Song na jihar Adamawa inda za’a rufe shi.
A rayuwarsa dai Farfesa AAmin likitan zuciya ne, sannan malami da shugaba Jami’ar Maiduri na Jahar bornin a wani lokaci, ya kuma karantar. Har’ila yau Farfesa Amin ya rike kujerar Ministan ilmi da manfetur, sannan jakadan Najeriya A Amurka sannan yan majalisar dattawa mai wakiltan Adama ta tsakiya.