Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta wallafa tsokacinta kan rahoton babban darartan Hukumar IAEA ga kwamitin gwamnonin hukumar

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta fitar da ra’ayoyinta da tsokacinta kan sabon rahoton da babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa (IAEA) ya gabatar ga kwamitin gwamnonin hukumar ta IAEA a ranar 24- wannan shekara ta 2025.

A cewar cibiyar diflomasiyya da ta yada labarai ta hukumar makamashin nukiliya ta Iran, an fitar da bayanin mai taken “Sa ido da Tabbatarwa a Jamhuriyar Musulunci ta Iran dangane da kudurin kwamitin tsaro mai lamba 2231 (2015)” a ranar 31 ga Mayu, 2025.

Bayanin ya fayyace cewa: Rahoton da babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa (IAEA) ya gabatar ga kwamitin gwamnoni mai taken: “Sabbin da tabbatarwa a Jamhuriyar Musulunci ta Iran bisa ga kudurin kwamitin sulhu mai lamba 2231 (2015)”.

Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana son bayyana ra’ayoyinta da tsakacinta  kan rahoton da babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa (IAEA) ya gabatar ga kwamitin gwamnonin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jamhuriyar Musulunci ta Iran makamashin nukiliya ta ga kwamitin

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Matakan Washington Na Hana ‘Yan Kasashen Musulmi Shiga  Amurka  Kiyayya Ce

Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ta bayyana cewa; Matakin da Amurka ta dauka na kakaba takunkumin  shiga Amurka akan wasu ‘yan kasa da kuma wasu kasashen musulmi yana nuni da yadda Amurkan take adawa da musulmi.

Haka nan kuma ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta ce; Daukin matakin hana wasu mutane yin tafiya saboda  kasar da su ka fito, ko addininsu yana nuni ne da yadda Amekin take jin fifiko da kuma nuna wariya.

A karshe ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta yi kira ga MDD da sauran cibiyoyin kasa da kasa na shari’a da su dauki mataki karara kuma a fili akan abinda Amurka ta yi, da ya sabawa duk wani ma’auni na ‘yan adamtaka.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne dai shugaban kasar Amurka Donald Trump ya rattaba hannu akan wata doka wacce ta hana ‘yan kasashe 12 shiga cikin Amurka, da kuma kafa tarnaki  akan wasu ‘yan kasashen 7. Fadar White House ta Amurka ta bayyana wannan matakin da ta dauka akan cewa; manufarsa shi ne kare tsaron kasar Amurka.

Kasashen da takunkumin shiga Amurkan ya shafa sun hada Afghanistan, Myanmar, Chadi, DRC, Equatorial Guinea, Eritria, Iran, Libya, Somaliya, Sudan da Yemen.

Su kuwa wadanda aka yi msu tarnaki ,sun kunshi  Brundi, Cuba, Laos, Saliyo, Togo, Turkimanestan da kuma Venezuela.

Shugaban na kasar Amurka ya kuma kara da cewa; Abu ne mai yiyuwa anan gaba a kara shigar da wasu kasashen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
  • Iran: Matakan Washington Na Hana ‘Yan Kasashen Musulmi Shiga  Amurka  Kiyayya Ce
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
  • Iran Ta Musanta Zargin Amurka Kan Cewa Kungiyoyi Masu Fada Ha HKI Suna Daukar Umurni Daga Wajenta Ne
  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin Zia Kawo Ziyara Tehran Nan Kusa
  • Sakon Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ga Mahajjatan Aikin Hajjin Bana A Kasa Mai Tsarki
  • Araghchi : Babu wata tattaunawa idan ba zamu tace uranium ba