UNICEF ya yi gargadi game da tabarbarewar matsalar jin kai a Gaza
Published: 8th, June 2025 GMT
Asusun Tallafawa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya yi gargadi game da tabarbarewar matsalar jin kai a zirin Gaza da Isra’ila ke ci gaba da yi wa kawanya.
Kakakin hukumar James Elder ya yi gargadin cewa, yara da dama da ke kwance a asibiti masu fama da matsananciyar yunwa ba za su iya rayuwa a mako mai zuwa ba idan har Isra’ila ta ci gaba da kafar ungulu da ayyukan jin kai a yankin.
A wata hira da yayi da gidan talabijin na Sky News, James Elder ya bayyana mummunan halin da ake ciki a Gaza da kuma sadaukarwar da iyaye mata suke yi don ciyar da ‘ya’yansu.
Wannan lokaci shi ne mafi wahala da mata da yara suka taba fuskanta a Gaza inji shi.
Ya ba da shaida ga yadda ya gamu da yaran da ke kwance a asibiti, wadanda rayuwarsu ke fuskantar barazanar rashin abinci mai gina jiki.
Rahotanni daga kungiyoyin da ke da alaka da Majalisar Dinkin Duniya da sauran hukumomin jin kai sun bayyana lamarin da mai ban tsoro.
Kungiyoyin ba da agaji sun yi gargadin cewa, idan ba a dage shingen da Isra’ila ta yi ba nan ba da jimawa ba, al’ummar kasar na cikin hadarin fadawa cikin wani bala’in jin kai da ba a taba gani ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya nemi sabbin hafsoshin tsaron ƙasar su zage damtse domin magance duk wata barazanar tsaro da ake fuskanta a halin yanzu da ma wadda ka iya kunnowa nan gaba.
Shugaban ya gargadi sabbin hafsoshin tsaron cewa ’yan Nijeriya sakamako kawai suke buƙata, ba uzuri ba, saboda haka dole ne su cika aikin da aka ɗora musu.
Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026 Ƙwallo ta kashe ɗan wasan CricketTinubu ya bayyana hakan ne bayan bikin ƙara wa sabbin hafsoshin tsaron da shugabannin rundunonin soji girma da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa yau Alhamis a Abuja.
A cewarsa, “Barazanar tsaro na ƙara sauyawa a kodayaushe, kuma abin da ya fi damun gwamnatinmu shi ne ɓullar sababbin ƙungiyoyin ’yan bindiga a Arewa ta Tsakiya, da Arewa maso Yamma, da wasu sassa a Kudanci.”
A ranar Laraba ce Majalisar Dattawa da ta Wakilai suka amince da naɗin Laftanar Janar Olufemi Oluyede a matsayin Babban Hafsan Tsaro; Manjo Janar Waidi Shaibu a matsayin Hafsan Sojan Ƙasa; Rear Admiral Idi Abbas Hafsan Sojan Ruwa; Air Marshall Kennedy Aneke Hafsan Sojan Sama; da Manjo Janar Emmanuel Undiendeye a matsayin Shugaban Tattara Bayanai na Soja.
“Ba zai yiwu mu ƙyale wannan sabuwar barazanar ta ci gaba ba. Dole ne mu ɗauki mataki da wuri. Mu sare kan macijin.
“’Yan Najeriya suna sa rana ganin sakamako, saboda haka babu wani uzuri da za su karɓa. Ina kuma kira da ku kasance masu dabaru da hangen nesa da kuma jarumta.
“Mu kasance mun tari hanzarin duk waɗanda ke neman tayar da zaune tsaye a ƙasarmu,” in ji Tinubu.
Yayin bikin, an ƙara wa Olufemi Oluyede muƙami zuwa Janar, Waidi Shaibu zuwa Laftanar Janar, Idi Abbas zuwa Vice Admiral, da Kevin Aneke zuwa Air Vice marshall, da kuma Emmanuel Undiendeye zuwa Laftanar Janar.