HausaTv:
2025-06-18@01:43:29 GMT

UNICEF ya yi gargadi game da tabarbarewar matsalar jin kai a Gaza

Published: 8th, June 2025 GMT

Asusun Tallafawa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya yi gargadi game da tabarbarewar matsalar jin kai a zirin Gaza da Isra’ila ke ci gaba da yi wa kawanya.

Kakakin hukumar James Elder ya yi gargadin cewa, yara da dama da ke kwance a asibiti masu fama da matsananciyar yunwa ba za su iya rayuwa a mako mai zuwa ba idan har Isra’ila ta ci gaba da kafar ungulu da ayyukan jin kai a yankin.

A wata hira da yayi da gidan talabijin na Sky News, James Elder ya bayyana mummunan halin da ake ciki a Gaza da kuma sadaukarwar da iyaye mata suke yi don ciyar da ‘ya’yansu.

Wannan lokaci shi ne mafi wahala da mata da yara suka taba fuskanta a Gaza inji shi.

Ya ba da shaida ga yadda ya gamu da yaran da ke kwance a asibiti, wadanda rayuwarsu ke fuskantar barazanar rashin abinci mai gina jiki.

Rahotanni daga kungiyoyin da ke da alaka da Majalisar Dinkin Duniya da sauran hukumomin jin kai sun bayyana lamarin da mai ban tsoro.

Kungiyoyin ba da agaji sun yi gargadin cewa, idan ba a dage shingen da Isra’ila ta yi ba nan ba da jimawa ba, al’ummar kasar na cikin hadarin fadawa cikin wani bala’in jin kai da ba a taba gani ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila

Kafofin yaɗa labarai na cikin gida a Iran sun yi iƙirarin cewa ƙasar ta kai hari kan hedikwatar hukumar leƙen asiri ta ƙasar Isra’ila (Mossad).

Kamfanin dillancin labaran Iran (TASNIM) ya ruwaito cewa rundumar juyin juya hali na Iran (IRGC) ce ta kai harin a hedikwatar Mossad da ke Herzliya.

Kamfanin ya wallafa wasu jerin hotuna da ya ce suna nuna yadda hedikwatar ta Mossad ke ci da wutan ne bayan harin makamai masu linzami ne da Iran ta kai mata.

Kafar yaɗa labarai ta Tehran Times ta ruwaito cewa hare-haren na IRGC sun ƙona wani ɓangare na cibiyar Aman, wanda wani ɓangare ne na ginin hukumar leƙen asirin asirin sojin Isra’ila ta Aman, da ke Glilot.

An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari

Kawo yanzu dai ba a iya tantance sahihancin wannan iƙirarin na Iran ba daga kafofin yaɗa labarai da ke aiki a yankin; kuma hukumomin Isra’ila ba su ce uffan a kai ba.

A cewar hukumar kare haƙƙin ɗan’Adam a Iran (HRANA), fararen hula 224 ne suka mutu, yayin da 188 suka jikkata a hare-haren Isra’ila a ƙasar.

HRANA ta kuma bayyana cewa sojoji 109 ne suka mutu inda kuma 123 suka jikkata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri
  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila