Burtaniya Ta Kakabawa Ministocin HKI Guda 2 Takunkuman Tattalin Arziki
Published: 11th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Burtaniya ta bada sanarwan kakabawa ministocin HKI guda biyu takunkuman tattalin arziki saboda ra’yinsu na wuce gona da Iri wanda zai bata duk wani shirin da kasashen duniya suke da shin a tabbatar da zaman lafiya a yanking abas ta tsakiya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kira-kirayen ministocin na kara mamaya da kuma korar falasdina daga yankin yamma da kogin Jordan ne yasa burtaniya ta nuki wannan batakin.
Bezalel Smotrich dai , wanda shi ne ministan kudi na HKI ya ce HKI zama kara mamayar yankin yamma da kogin Jordan, kafin zaben shekara ta 2026, sannan ya rantse kan cewa za’a share falasdinawa a gaza, kuma zasu wargaza kungiyar Hamas a cikin yan watanni masu zuwa.
Sannan Itamar Ben-Gvir kuma wanda ya kasance ministan harkokin yakin kasar ya bukaci a kara ginawa gidaje sannan a fadada kai hare-hare a kan falasdinawa ta yadda nan gab aba wanda zai sake maganar warware rikicin gabas ta tsakiya ta hanyar kafa kasashe biyu.
Takunkuman tattalin arziki zai iya tada jijiyoyin wuya a tsakanin kasashen biyu amma kuma ba zasu hana HKI yin abinda ta ga dama ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa, a halin yanzu Jamhuriyar Musulunci za ta iya kai wa Isra’ila hari “daidai” inda ta ke so bayan samun bayanan sirri kan cibiyoyin nukiliyar gwamnatin Isra’ila.
Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wata wasika mai zuwa ga ministan leken asirin kasar, Esmail Khatib, inda ya taya shi murnar wani samame da aka kai a kwanan baya wanda ya bayar da damar samun bayyana sirrin Isra’ila da dama kan shirinta na nukiliya.
Wannan nasarar, ta baiwa hukumomin leken asirin Iran damar samun wasu tarin takardun Isra’ila da suka shafi makaman nukiliya, soji, tsaro da wasu wurare na kayayyakin more rayuwa.
Wuraren sun hada da wuraren da Isra’ila ke da shirin nukiliyar gwamnatin na boye, wanda aka ce ya baiwa Tel Aviv damar kera daruruwan makamai masu linzami da ba a san da su ba.
Janar Salami ya kara da cewa: “Wadannan takardun sirrin babu shakka zasu inganta tasirin kokarin da ake yi na hanzarta kawar da gwamnatin Sahayoniyawan da kuma kara sahihancin harin makamai masu linzami na Iran.
A shekarar da ta gabata Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kai hari kan wasu muhimman wurare na Isra’ila a yankunan Falasdinawa da ta mamaye a wani gagarumin farmakin ramuwar gayya da ta gudanar a matsayin mayar da martani ga wuce gona da iri na gwamnatin Isra’ila.