Aminiya:
2025-07-29@05:10:08 GMT

An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

Published: 12th, June 2025 GMT

Aƙalla mutum huɗu ciki har da jaririn wata tara aka kashe a wani hari da aka kai ƙauyen Nkiendowro da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Mutanen da suka rasu sun haɗa da mata biyu da namiji ɗaya, wanda aka ce suna aikin jigilar kwashe tumatir daga ƙauyen zuwa kasuwar Farin-Gada da ke Jos lokacin da aka kai musu hari.

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Wasu mutum biyu kuma sun jikkata a harin, wanda yanzu haka suna karɓar magani a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.

Shugaban tsaron al’ummar Miango, Josiah Zongo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin, yayin da waɗanda suka jikkata ke karɓar kulawa.

Rundunar ’yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba kan harin.

A wani lamari makamancin haka, an kai hari ƙauyen Murish da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a daren ranar Laraba, amma matasa da mazauna ƙauyen sun yi nasarar kare kansu daga maharan.

Wani matashi daga ƙauyen ya bayyana cewa maharan sun shigo suna harbi, amma mutanen ƙauyen sun kare kansu.

Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar Mwaghavul Development Association kuma shugaban sansanin ‘yan gudun hijira a Mangu, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu cikin lumana.

Ƙananan hukumomin Mangu da Bassa sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al’umma game da tsaro a Jihar Filato.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari

এছাড়াও পড়ুন:

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Masu karatu za su so jin dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a garin Gombe, amma sai daga bisani na bar garin Gomben da zama na dawo Kano, tun ina ‘yar shekara biyar da haihuwa, sakamakon mahaifina yana aiki a Kanon. Kazalika, na girma a gaban iyayena, na yi firamare da sakandare duk a garin Kano, sannan kuma ban taba yin aure ba; budurwa ce ni.

 

Wace irin rawa kike takawa a cikin masana’antar shirya finafinai ta Kannywood?

Ina fitowa ne a matsayin Jaruma kawai, amma kuma ina da niyyar zama mai bayar da umarni a nan gaba kadan insha Allah.

 

Me ya ja hankalinki, har kika tsunduma harkar fim?

Wato batu na gaskiya, fim yana burge ni kwarai da gaske, amma dalilin shigata sana’ar ita ce; wani fim aka yi sai wata arniyya ta musulunta, daga nan ne na ce; in dai har fim yana isar da sako, har ya zama silar gyaruwar al’umma, gaskiya zan zama daya daga cikin wadanda za su isar da wannan sako, tunda da ma raina yana so matuka gaya.

 

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?

Gaskiya ni ban sha wahala ba, dalili kuwa shi ne; dan fim ne ya sa ni a harkar ta fim, sannan kuma kamar yaya yake a wajena, dan Unguwarmu ne, iyayena da nasa sun zama kamar ‘yan’uwa.

 

Lokacin da kika fara sanar wa iyayenki cewa, kina son shiga harkar fim, wane kalubale da kika fuskanta daga wurinsu? 

Eh! Gaskiya na fuskanci kalubale, amma daga baya sun fahimce ni, sakamakon iyayen nawa masu fahimta ne.

 

Za ki yi kamar shekara nawa da fara fim?

Ina ga zan samu kamar shekara takwas da farawa.

 

Ya farkon fara dora miki Kyamara ya kasance?

Ban ji tsoron komai ba, kuma Alhamdulillahi na samu yabo sosai daga wajen masu bayar da umarni da sauran abokan aiki.

 

Wane fim kika fara yi a farkon zuwanki?

Na fara ne da fim din Dadin Kowa.

 

Wace rawa kika taka a cikin shirin na Dadin Kowa?

Na fito ne matsayin Sailuba, inda na taka rawa a matsayin matar aure. Surukata ce ta auro wa mijina ni a kauye, saboda ba ta son matar dan nata da aura, sakamakon cewa; Beyerabiya ce, wato maman Rasaki kenan, ni kuma a nan na yi ta tsula tsiyata.

 

Bayan da aka fara haska fuskarki cikin shirin Dadin Kowa, ya kika ji a lokacin, sannan kuma yaya kika kasance da mutanen Unguwarku da sauran ‘yan’uwa?

Alhamdulillah! Wadanda suka san ni a gaske, sun biyo ni har gida suna kallona kamar a da ba su san ni ba, wadanda kuma ba su san ni ba, idan muka hadu abin ba dama, ga tarin alhairai daga masoya daga gurare daban-daban.

 

Bayan shirin Dadin Kowa da kika fito a ciki, ko akwai wasu fina-finan da kika fito ciki?

Eh, na yi wasu fina-finan da dama.

 

Kamar wadanne kenan?

Kamar irin su: Ni da Mijin Yayata, Matar Waye, Zaman Tare, Matar Kaddara da dai sauransu, dukkanninsu masu masu dogon zango ne kuma ni ce jarumar ciki.

 

Cikin wadannan fina-finai da kika zayyano, wane fim ne ya fi burge ki, kuma me yasa, sannan wace rawa kika taka a cikin shirin?

Ni da mijin Yayata, na fito ne a matsayin budurwa wacce take matukar son mijin yayarta.

 

Ya kika ji a lokacin da za ki taka rawa a wannan shirin?

Na ji dadi sosai, saboda zan yi abin da nake so; sannan kuma an kara min kwarin gwiwa, har muka yi muka gama babu wata matsala.

 

Ya batun masu kallo bayan shirin ya fita, ko kin samu wani kalubale daga gare su?

A a, kawai dai idan aka gan ni a zahiri, a kan yi mamaki tare da bayyana cewa; na fi kyau a fili, wasu ma har su ce ba su yi zaton cewa; ‘yar birni ba ce ni, sun yi zaton yadda nake ‘yar kauye a Dadin Kowa, a gaske ma haka nake.

 

A fina-finan da kika yi, wane fim ne ya fi haska ki; har mutane suke iya gane ki?

Dadin Kowa, sai kuma wannan fim din na Matar Waye, shi ma ba abin da zan ce gaskiya.

 

Ko akwai wani kalubale da kika taba fuskanta, tun daga farkon zuwanki cikin masana’antar zuwa yanzu?

Gaskiya an samu, amma a da ne; yanzu cikin ikon Allah an samu daidaito.

 

Wadane irin nasarori kika samu game da fim?

Akwai nasarori da dama kamar ta fuskar samun kudi, mota, kayan sakawa, turaruka da sauran makamantansu.

 

Ko kina da ubangida a masana’antar Kannywood?

Kwarai da gaske ina da su, akwai Adam Musa Adam da kuma Usman Adam Hali Dubu.

 

Kafin ki fara fim, wadane jarumai ne suka fi burge ki har kike jin dama ki zama tamkar su?

Ina kowace jaruma, domin kuwa dukkaninsu suna burge ni.

 

Yaushe kike sa ran yin aure?

Duk lokacin da Allah ya kawo shi, a shirye nake.

 

Ko akwai wanda ya taba cewa yana son ki zai aure ki a masana’antar?

Kwarai da gaske, akwai.

 

Ko za mu iya jin sunansa?

A’a gaskiya.

 

Mene ne ra’ayinki game da auren dan fim?

Zan iya aurensa mana, ai babu wata matsala a ciki.

 

Wane irin namiji kike so ki aura?

Ya kasance Musulmi, mai ilimi, wanda kuma yake da cikakkiyar sana’a.

 

Wace shawara za ki bai wa abokan aikinki na masana’antar Kannywood?

Da farko dai, ya kamata mu hada kanmu, sannan mu kiyaye abin da zai bata sunan sana’ar tamu, mu kuma yi kokari wajen kare mutuncinmu, wannan shi ne a takaice.

 

Wacce shawara za ki bawa masu kokarin shigowa wannan masana’anta?

Su tabbata sun shigo da niyya mai kyau, sannan kuma su yarda cewa; sana’a suka zo yi, ba wani abu daban ba.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Ina fatan alhairi ga kowa da kowa, musamman masoyana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana
  • Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
  • Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN
  • Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji
  • Duk da kashe jagororin ’yan bindiga, Turji na ci gaba da kai hare-hare