Aminiya:
2025-09-17@23:28:33 GMT

An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

Published: 12th, June 2025 GMT

Aƙalla mutum huɗu ciki har da jaririn wata tara aka kashe a wani hari da aka kai ƙauyen Nkiendowro da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Mutanen da suka rasu sun haɗa da mata biyu da namiji ɗaya, wanda aka ce suna aikin jigilar kwashe tumatir daga ƙauyen zuwa kasuwar Farin-Gada da ke Jos lokacin da aka kai musu hari.

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Wasu mutum biyu kuma sun jikkata a harin, wanda yanzu haka suna karɓar magani a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.

Shugaban tsaron al’ummar Miango, Josiah Zongo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin, yayin da waɗanda suka jikkata ke karɓar kulawa.

Rundunar ’yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba kan harin.

A wani lamari makamancin haka, an kai hari ƙauyen Murish da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a daren ranar Laraba, amma matasa da mazauna ƙauyen sun yi nasarar kare kansu daga maharan.

Wani matashi daga ƙauyen ya bayyana cewa maharan sun shigo suna harbi, amma mutanen ƙauyen sun kare kansu.

Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar Mwaghavul Development Association kuma shugaban sansanin ‘yan gudun hijira a Mangu, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu cikin lumana.

Ƙananan hukumomin Mangu da Bassa sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al’umma game da tsaro a Jihar Filato.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara