Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
Published: 12th, June 2025 GMT
Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Manjo Janar Hussain Salami ya fada a yau Alhamis cewa; Abokan gaba suna yi mana barazana da yaki, sannan ya tabbatar da cewa a shirye suke su fuskanci duk abinda zai faru.
Manjo janar Salami wanda ya gabatar da jawabi ga taron dakarun sa-kai na “Basiji a nan Tehran ya kuma kara da cewa; Babu wani wuri komai zurfi da nisansa a HKI da ba mu tsinkayowa, idan kuwa aka ba mu umarni to za su yi nasara, mu Sanya abokin gaba ya yi nadama.
A gefe daya ministan tsaron Iran ya bayyana cewa; Duk wani hari da ake tunanin kawo wa Iran, to kuwa zai fuskanci mayar da martani mai tsanani.
Ministan tsaron na Iran Laftanar janar Azizi Nasri Zadeh ya kara da cewa; Idan har yaki ya barke, to za a tilasta wa Amruka ficewa daga wannan yankin, kuma asarar da za ta yi sai ta rubanya wacce za ta yi wa Iran.”
Ministan tsaron na Iran ya kuma ce; Abin takaici ne yadda wasu jami’an Amurka su ka yi barazanar yiyuwar barkewar yaki, idan ba a cimma matsaya ba a tattaunawar Nukiliya, sannan ya kara da cewa: Tehran ba ta maraba da yaki, amma kuma a lokaci daya ta shirya masa.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
Al’ummar Iran masu daraja!
Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.
Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.
A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.
Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.
Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.