Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian ya bayyana shirin kasarsa na samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin kasaahen Pakistan da Indiya.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif a ranar Asabar.

Shugaban na Iran ya ce manufar Iran ta mayar da hankali ne kan inganta samar da zaman lafiya a duniya musamman a cikin kasashen musulmi.

Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci tana maraba da duk wani mataki da kokarin samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin Pakistan da Indiya, kuma za ta iya taka rawar shiga tsakani ga wannan manufar.”

A nasa bangaren firaministan kasar Pakistan ya mika sakon gaisuwar babba salla da sakon fatan alheri ga al’ummar Iran da kuma jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Sharif ya kuma bayyana fatan ganin an aiwatar da yarjejeniyoyin kasashen biyu da Pakistan da Iran suka kulla.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: samar da zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 

Kamfanonin wutar lantarki sun yi barazanar katse wutar a fadin Najeriya saboda tarin bashin da ya haura Naira tiriliyan 5.2 da suke bin gwamnati.

Taurin bashin, wanda ke barazana ga ci gaba da ayyukan kamfanoni, ya hada da Naira tiriliyan 1.2 na wutar da aka samar a watanni shidan farkon shekarar 2025, da Naira tiriliyan 2 daga 2024, da kuma bashin da aka gada tun daga 2015 wanda ya kai Naira tiriliyan 1.9.

Shugabar ƙungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ta bayyana cewa kamfanonin sun daɗe suna nuna kishin ƙasa ta hanyar ci gaba da samar da wuta duk da rashin biyan su kuɗaɗensu, amma yanzu sun gaji.

Ta bayyana cewa kudin da ake kashewa wajen samar da wuta a kowane wata yana kaiwa Naira biliyan 250, amma Gwamnatin Tarayya ta ware Naira biliyan 900 kacal a kasafin kuɗin 2025, kuma har zuwa yau ba a samu cikakken tabbacin samun wannan kuɗin ba.

An rufe masana’antu 1,724 bisa rashin bin dokokin aiki a Guinea NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa

Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa gwamnati tana ƙoƙarin rage wani ɓangare na bashin, amma har yanzu ba a bayyana yadda hakan zai faru ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar