Sai dai Bukar ya musanta wannan iƙirari, yana mai cewa ya sanar da shugabansa kuma ya bi duk matakan da suka dace, amma har yanzu ba a bi masa haƙƙinsa ba. Ya ce sau da dama an buƙaci ya kawo bayanan asusun ajiyarsa na banki don duba matsalarsa, amma babu wani canji. Duk da cewa shugaban makarantar ya wanke shi daga zargin guduwa daga aiki, har yanzu ba a mayar masa da albashinsa ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Bukar

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina

A wasu yankunan Jihar Katsina da suka daɗe cikin fargaba da hare-haren ’yan bindiga, zaman lafiya ya fara dawowa sakamakon sulhu da al’umma suka yi da masu tayar da ƙayar baya.

Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin daminar bana.

Manoma sun fara noma cikin kwanciyar hankali

Ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da Ɗanmusa na daga cikin wuraren da aka samu wannan ci gaba. Wasu manoma da wakilinmu ya zanta da su sun bayyana farin cikinsu da yadda rayuwa ke dawowa dai-dai.

Malam Rabe, manomi daga Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma na fi shekara 8. Amma yanzu gashi ni ne har da yin ɓaɓar shanu.”

Ya ƙara da cewa:  “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani. Rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, Gangara, Zandam da sauran yankuna.”

Sulhu da ’yan bindiga ya sauya fasalin rayuwa

Alhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce:  “Mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”

A cewar Surajo, hatta tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, ya koma noma.

“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”

Noman kankana ya kankama a Jibiya

Malam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce:  “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”

Koyi da Batsari aka yi

A Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce:  “Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”

Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”

Da sauran rina a kaba

Duk da wannan ci gaba, wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur na ci gaba da fuskantar hare-hare. A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.

Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun ɓar gonakin saboda tsoron hare-hare.

 

A cikin ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da ƊanMusa da ke Jihar Katsina, al’umma sun ɗauki matakin da ba a saba gani ba — sun yi sulhu da ’yan bindigar daji, waɗanda suka daɗe suna addabar yankin da garkuwa da mutane, kisan gilla da satar shanu.

Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya fara haifar da zaman lafiya da ci gaba.

Manoma sun koma gona

Manoman yankin sun fara komawa gonakinsu cikin daminar bana, suna noma ba tare da fargaba ba. Wasu daga cikinsu sun bayyana cewa sulhun ya kawo sauyi mai ma’ana.

Malam Rabe, wani manomi daga garin Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma gaskiya na fi shekara 8, ko in ce 10. Amma yanzu gashi ni ne har da yin huɗar shanu.”

Ya ƙara da cewa:  “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani a cikin gonar. Ka san daga bisani rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, ka tafi har can wajen su Gangara da su Zandam da sauran waɗannan yankuna.”

Sulhu ya canza rayuwa

Alhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce: “Lallai mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta da cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”

Abin ban mamaki shi ne, tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, shi ma ya koma noma.

“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”

Noman kankana ya kankama a Jibiya

Malam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce: “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”

Batsari ta fara, sauran na bi

A Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce:

“Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”

Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”

Da sauran rina a kaba

Ƙaramar Hukumar ƊanMusa ta baya-bayan nan ce da ta yi sulhu, kuma ana ganin tasirinsa. Sai dai a wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur, harin ’yan bindiga bai tsaya ba.

A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.

Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun bar gonakin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
  • Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure
  • Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”
  • CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD
  • Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
  • An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
  • NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
  • Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
  • Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal
  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu