Nijeriya Ta Fuskanci Cikas Wajen Karɓo Rancen Dala Biliyan 5 Daga Saudiyya
Published: 11th, June 2025 GMT
Amma har zuwa yanzu, babu cikakken bayani daga Gwamnatin Tarayya.
A watan Mayun 2025 ne Tinubu ya miƙa buƙatar samun amincewar majalisa domin karɓar rancen Dala biliyan 21 daga ƙasashen waje, ciki har da Dala biliyan biyar daga Aramco.
Rahoton Reuters bai bayyana sunayen bankunan da za su taimaka ba, amma majiyoyi sun ce ɗaya daga cikin bankunan na nahiyar Afrika ne, sauran kuma daga Gabas ta Tsakiya.
Idan aka cimma yarjejeniyar, wannan zai zama mafi girma daga cikin bashin da Nijeriya ta taɓa karɓa a irin wannan hanya daga Saudiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya Rance Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Sake Tunzura Iran Shirin Makamashin Nukiliyarta Zai Fuskanci Martani
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Sake kunna ‘hanyar tayar da hankali’ zai gamu da martani mai ƙarfi na Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Fitar da kudiri kan Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta yi ba zai shafi kudurin al’ummar Iran ba ko kuma ci gaban shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya.
A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Iran a yammacin ranar Talata, Baqa’i ya yi la’akari da dukkanin rahotanni da kudurorin da suka shafi siyasa. Ya kuma kara da cewa Iran ba ta keta hurumin da ya rataya a wuyanta ba, kuma kasashen yammacin turai suna dora barazanarsu ne kan zargin da aka shafe shekaru 20 ana yi. Ya jaddada cewa Iran ba za ta yi watsi da hakkinta na inganta sinadarin Uranium ba.
Ya yi nuni da cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, Rafa’el Grossi, yana aiki ne da son zuciya, da kuma maimaita labaran bangarorin da ke adawa da Iran, ya kara da cewa, mayar da “hanyar tayar da hankali” za ta fuskanci martani mai karfi na Iran.
Dangane da matsayin Sanya batun Iran a gaba a hukumar ta IAEA da kuma barazanar da kasashen Turai ke yi na fitar da wani kuduri a taron majalisar alkalan hukumar IAEA da ke gudana a halin yanzu, ya bayyana cewa, batun nukiliyar Iran wani kuduri ne na siyasa kawai tun da farko, a lokacin da ya shiga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kuma kafin nan, lokacin da ake kallon lamarin a matsayin wani lamari mai yaduwa.