HausaTv:
2025-06-13@12:12:15 GMT

Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242

Published: 12th, June 2025 GMT

Hukumomi a India sun ce da yiwa a samu wanda ya tsira daga hatsarin jirgin samanAir India da ya faru a yau Alhamis.

Jirgin samfarin Boeing 787 Dreamliner wanda ya tashi Ahmedabad zuwa birnin Landan ya yi hatsari jim kadan bayan tashinsa dauke da fasinjoji 242 da ma’aikatan jirgin inji kamfanin air India.

Bayanan farko da kamfanin na Indiya ya fitar sun ce akwai, Indiyawa 169, ‘yan Burtaniya 53 da, ‘yan  Portugal 7 sai dan Canada guda a cikin jirgin. Kuma babu wanda ya tsira, a cewar shugaban ‘yan sandan Ahmedabad.

Hukumomin India da na Ingila da Portigal duk sun jajanta game da mummunan hatsarin.

Jami’an kashe gobara a arewa maso yammacin Indiya tun da farko sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa wani jirgin sama ya fado a filin jirgin.

Hotunan farko da aka watsa a gidajen talabijin na Indiya sun nuna wani jirgin sama yana shawagi a wata unguwa, kafin ya bace wurin ya turnuke da bakin hayaki.

Bayanai sun ce wannan shi ne hatsarin farko na jirgin Boeing 787 Dreamliner wanda ya fara aiki a shekarar 2011.

Kamfanin Boeing ya ce tuni ya fara tattara bayanai don sanin hakikanin abinda ya faru.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

Binciken ya nuna cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin ma’aikatan Dangote ne kai tsaye, yayin da sauran ke aiki da kamfanonin da ke da alaka da safarar mai daga matatar Dangote zuwa wuraren ajiya na kamfanin da ke Ibese da Obajana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4
  • Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4
  • Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya
  • Gidauniyar Hind Rajab ta kai karar Isra’ila kan harin jirgin ruwan Madleen
  • Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza