Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya nanata matsayin Taiwan da jaddada manufar Sin daya tak a duniya yayin tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Faransa Jean-Noel Barrot a jiya Jumma’a. Ya kuma bayyana adawar Sin da shigar kungiyar tsaro ta NATO cikin harkokin yankin Asiya da Pasifik.

Wang Yi wanda mamba ne na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya nanata cewa, batun da ya shafi Taiwan, batu ne na cikin gidan Sin da ya shafi ’yancin kasar da iko kan yankunanta, wanda ya bambanta da batun kasar Ukraine.

Ya ce Sin na daukar amincewa da manufar kasar daya tak da Faransa ta yi da muhimmanci, kuma tana fatan ganin hakan a aikace.

Bugu da kari, ministan ya bayyana fatan Sin na ganin Faransa ta rike matsayin da ya dace da adawa da shigar NATO cikin harkokin Asiya da Pasifik tare da jaddada cewa, ya kamata kasashen biyu su inganta cudanyar bangarori daban daban da kare tsarin ciniki cikin ’yanci da adawa da ayyukan cin zali.

A nasa bangare, Jean-Noel Barrot ya ce Faransa za ta ci gaba da daukar Sin a matsayin kawa kuma abokiyar hulda, da nace wa manufar Sin daya tak tare da sa ran ci gaba da aiwatar da musaya tsakanin manyan jami’ansu da tuntuba ta kut da kut bisa manyan tsare-tsare tsakaninta da Sin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yau mutane na kallon bukukuwan Sallah da ido daban—yayin da wasu ke ganin ta zama lokaci na shakatawa nishadi kawai, wasu kuwa na cewa an bar al’adun da ke nuna kimar wannan babban lokaci na Musuluncin.

 

Wadanda suka manyanta na ganin akwai abubuwa da dama da a yanzu matasa sukayi watsi da su wadanda kuma na da muhimmanci yayin bukukuwan sallah a da can baya wanda kuma suke ganin ba a yin su a yanzu.

Ko wadanne irin al’adu kenan na bukuwan sallah da dattawa ke ganin anyi watsi dasu.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan yadda aladun bukukuwan Sallah ke canzawa a wannan zamani.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
  • 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce
  • Kasar Faransa Ta Jaddada Aniyarta Ta Amincewa Da Yantacciyar Kasar Falasdinu
  • Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah
  • Bukukuwan sallah tare da Malta Guinness a Birnin Kano
  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
  • Araghchi : Babu wata tattaunawa idan ba zamu tace uranium ba