Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Published: 8th, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya nanata matsayin Taiwan da jaddada manufar Sin daya tak a duniya yayin tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Faransa Jean-Noel Barrot a jiya Jumma’a. Ya kuma bayyana adawar Sin da shigar kungiyar tsaro ta NATO cikin harkokin yankin Asiya da Pasifik.
Wang Yi wanda mamba ne na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya nanata cewa, batun da ya shafi Taiwan, batu ne na cikin gidan Sin da ya shafi ’yancin kasar da iko kan yankunanta, wanda ya bambanta da batun kasar Ukraine.
Bugu da kari, ministan ya bayyana fatan Sin na ganin Faransa ta rike matsayin da ya dace da adawa da shigar NATO cikin harkokin Asiya da Pasifik tare da jaddada cewa, ya kamata kasashen biyu su inganta cudanyar bangarori daban daban da kare tsarin ciniki cikin ’yanci da adawa da ayyukan cin zali.
A nasa bangare, Jean-Noel Barrot ya ce Faransa za ta ci gaba da daukar Sin a matsayin kawa kuma abokiyar hulda, da nace wa manufar Sin daya tak tare da sa ran ci gaba da aiwatar da musaya tsakanin manyan jami’ansu da tuntuba ta kut da kut bisa manyan tsare-tsare tsakaninta da Sin. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe
A yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce hadaddiyar sanarwar da aka fitar a gun taron ministocin harkokin waje na kungiyar G7 ba ta da tushe, inda ta zargi kasar Sin, ta kuma tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasar. Don haka Sin ba ta amince da sanarwar ba.
Rahotanni na cewa ministocin harkokin wajen kasashe membobin kungiyar G7, sun tattauna damuwar da ake nunawa game da fadada karfin soja, da makaman nukiliya na kasar Sin, inda suka ce suna bukatar bangaren Sin ya yi alkawarin kiyaye zaman lafiya.
Game da hakan, Lin Jian ya ce Sin kasa ce da ta fi mayar da hankali ga batun kiyaye zaman lafiya da tsaro, tana kuma tsayawa tsayin daka kan turbar samun ci gaba cikin lumana, da manufofin kiyaye tsaron kasa, da na kiyaye takaita yawan makaman nukiliya bisa bukatun tsaron kasar.
ADVERTISEMENTJami’in ya ce kungiyar G7 ba ta ambato alhakin dake wuyan kasar Amurka, na rage makaman nukiliya, da hadarin yaduwar makaman nukiliyar a sakamakon raya dangantakar abota, ta kiyaye tsaro a tsakanin Amurka da Birtaniya da Australia ba, amma ta zargi kasar Sin ba tare da wani tushe ba. (Zainab Zhang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA