Kasar Rwanda Ta Fice Daga Cikin Kungiyar Tattalin Arziki Ta Tsakiyar Afirka
Published: 9th, June 2025 GMT
A daidai lokacin da kungiyar kasashen tsakiyar Afirka ta tattalin arziki ( ECCAS) take yin taro, kasar Rwanda ta sanar da ficewa daga cikinta.
Bayanin da gwamnatin kasar ta Rwanda ta fitar ya kunshi cewa; Kasar Rwanda tana nuna takaicinta akan yadda kasar DRC take amfani da kungiyar tattalin arziki ta tsakiyar Afirka a matsayin wani makamin a hannunta.
Bayanin gwamnatin ta Rwanda ya kara da cewa: Yadda DRC take amfani da wannan kungiyar ya sake fitowa fili a yayin taron kungiyar karo na 26 a Malabo, ta yadda aka kau da kai akan hakkin Rwanda na shugabancin karba-karba,kamar yadda yake a cikin doka ta shida ta kundin kungiyar. Hakan kuma ya faru ne sanadiyyar shiftar DRC ga kungiyar.”
A yayin da aka shirya cewa a shekara mai zuwa kasar ta Rwanda za ta karfi shugabancin kungiyar, jami’an kasar DRC sun ce, ba za su sami halartar taron da za a yi a kasar ta Rwanda ba.
Kasashen biyu dai suna zaman tsami bisa zargin da Kinshasa take yi wa Kigali na cewa tana goyon bayan kungiyar ‘yan tawaye ta M23.
Yanzu dai kungiyar ta ECCAS tana da mamabobi 11 bayan ficewar kasar Rwanda. Kasashen su ne: Angola, Burundi, Cameroon, Afirka Ta Tsakiya,c, Congo, Gabon, Equatorial Guinea, Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, Rwanda, Sao Tome, sai tsibirin Principe da Chad.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Rwanda
এছাড়াও পড়ুন:
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Ma’aikatar kula da harkokin waje da cinikayya ta Namibia ta ce kasar za ta yi amfani da baje kolin cinikayya da tattalin arziki na Sin da Afrika (CAETE), wanda za a yi a lardin Hunan na kasar Sin, wajen zurfafa hadin gwiwa da Sin da lalubo sabbin damarmakin samun ci gaba.
Ma’aikatar ta bayyana haka ne cikin wata sanarwar da ta fitar jiya, inda ta bayyana cewa zuwa baje kolin ya nuna kudurin kasar na karfafa hadin gwiwa da dukkan abokan huldar samun ci gaba da na cinikayya, wadanda za su samar da damarmakin ga al’umma da sanya Namibia zama mai taka rawa a harkokin raya shiyyarta da ma nahiyar Afrika.
Sanarwar ta kara da cewa, Namibia za ta shiga cikin kasashe manyan baki a baje kolin CAETE na 4 da za a shirya a birnin Changsha na lardin Hunan, daga ranar 12 zuwa 15 ga watan Yuni. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp