More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Asibiti ko dakin shan magani ko wani bigire mai kama da wadannan wuri ne da marasa lafiya kan je ko ake kai su don neman waraka a duk lokacin da bukatar haka ta taso.

Wuri ne da akan ware domin ceto rayukan wadanda suka jikkata suke kuma bukatar agajin gaggawa.


A bisa al’ada kuma, ana sa ran samun tausayi da jinkai da sadaukarwa wajen yin dukkan mai yiwuwa kuma a ko wane lokaci don ceton rayuka daga jami’an lafiya.
Sai dai ’yan Najeriya da dama sun dade suna kokawa da yadda a cewarsu wasu jami’an kiwon lafiya kan nuna halin ko-in-kula, a wasu lokutan ma da sakaci, wanda kan kai rasa rayuka.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah

Shirin Daga Laraba na wannan mako zai zube komai a faifai don gano sahihancin wannan zargi da ’yan Najeriya suke yi da kuma, idan zargin ya tabbata, yadda aikin jami’an lafiya ya yi hannun riga da abin da aka karantar da su.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jami an kiwon lafiya Marasa Lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Jiya Juma’a an kammala zagayen karshe na gasar kirkire-kirkire, ta daliban kasa da kasa ta kasar Sin ta yankin Afirka a birnin Nairobin kasar Kenya, wadda jami’ar koyon ilmin aikin gona ta Nanjing ta kasar Sin ta karbi bakuncin shiryawa. Wannan shi ne karon farko da aka gudanar da gasar a nahiyar Afirka.

Rahotanni na cewa, an gudanar da gasar ne a tsawon kwanaki biyu, kuma dalibai 559 daga jami’o’in Afirka 115 sun yi rajitar halartar gasar, kana an baje kayayyakin shiga gasar har 185, wadanda suke shafar fasahohin aikin noma da abinci, da amfani da basirar AI, da kiyaye muhalli, da samun ci gaba mai dorewa da sauransu.

A karshe, alkalan gasar sun tattauna, tare da tsai da kudurin bayar da lambobin yabo ga tawagogi 30 na jami’o’i 21 daga kasashe 9. A cikinsu, tawagar jami’ar Egerton ta kasar Kenya, ta samu lambar yabo ta zinari bisa aikin da ta gabatar na dasa tsiron tumatir a jikin wata bishiya ta daban.

Mataimakiyar shugaban jami’ar koyar da ilmin aikin gona ta Nanjing Zhu Yan, ta bayyana cewa, an gudanar da gasar kirkire-kirkire ta daliban kasa da kasa ta kasar Sin ta yankin Afirka karo na farko ne, don sa kaimi ga matasan Sin da Afirka, da su yaukaka mu’amalar al’adu da juna, da kokarin yin kirkire-kirkire tare, da kuma nazarin samar da ci gaba mai dorewa tare. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF
  • ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David Mark
  • Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
  • Mutane 6 Ne Suka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Yan Ta’adda A Zahidan
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta
  • ALGON Ta Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da NUJ Don Inganta Kwarewar Aiki
  • Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma
  • NAJERIYA A YAU: Yadda masu yi wa kasa hidima za su ci arzikin yankunan da suke aiki