’Yar gudun hijira ta haifi ’yan 4 a Benuwe
Published: 10th, June 2025 GMT
Wata mata, Shidoo Tortiv da ta tsere daga matsugunninta sanadiyyar matsalar tsaro ta haifi ’yan huɗu a gidan ’yan uwa da take zaman gudun hijira a Jihar Benuwe.
Shidoo Tortiv wadda ta fito daga ƙauyen Ucha na Ƙaramar Hukumar Gwer ta Yamma sun tsere tare da mijinta, Wilfred Tortiv sakamakon matsalar tsaro da ta yi kamari, inda suka nemi mafaka a gidan ’yan uwansu.
Mista Wilfred Tortiv Mijin matar ya shaida wa wakilinmu a ranar Litinin cewa ta haifi jariran ne da misalin karfe 6 na yammacin ranar Asabar a gida bayan nakuda ta kama ta kuma ungozomai suka karbi haihuwar saboda babu lokaci da kuma kudin kai ta asibiti.
Ya bayyana cewa wannan ce haihuwa ta uku da matarsa ta yi kuma duk ’ya’yanta na farko da na biyu maza, sai dai wannan da aka samu maza biyu da mata biyu, lamarin da ya ce dawainiyarsu za ta kara musu matsin rayuwa.
Tuni dai Gwamna Hyacinth Alia ya bayar da umarni mika matar da yayan da ta haifa zuwa Asibitin Koyarwa na Jamiar Benuwe da ke Makurdi domin samun kulawar da ta dace.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gabon: An Daure Mata Da ‘Dan Tsohon Shugaban Kasa Bongo Shekaru 20 A Gidan Yari
Matar tsohon shugaban kasar Gaba, Sylvia Bongo da kuma dansa Nuruddin Bongo za su yi zaman kaso na tsawon shekaru 20 saboda samunsu da laifin almubazzaranci da kudin kasa.
Kotun da ta yi shari’ar ta yanke hukunci ne akan iyalan tsohon shugaban kasar Ali Bongo ba tare da suna gabanta ba. Kotun dai an kafa ne domin yin binciken laifuka da suke da alaka da barnata dukiyar kasa.
Kotun ta sami mai dakin tsohon shugaba Bongo, Sylvia Bongo Ondimba da laifin almundahana da dukiyar kasa da kuma yin takardu na jabu.
Shi kuwa Nuruddin Bongo an same shi ne da laifukan da su ka hada da runton bai wa kai mukamai,wanke kudaden haram da mayar da su halaliya, sannan da shirya makarkashiya domin aikata laifuka.
Kowane daya daga cikinsu an kuma ci tararsu da kudin da sun kai saifa miliyan 100.
Dan shugaban kasar ta Gabon Nuruddin Bongo ya kore cewa ya yi almundahanar kudin kasar, kuma ya yi alkawalin ci gaba da kare hakkinsa har bayyanar gaskiya.
Mai shigar da kara na gwamnati ya bukaci ganin kotun ta musamman ta yanke wa Sylvia da Nuruddin hukuncin zaman kurkuku na shekaru 20, saboda daukar duniyar al’umma da mayar da ita ta kashin kai.
A 2023 ne dai aka yi juyin Mulki a kasar ta Gabon wanda ya kawo karshen mulkin iyalan Bongo na tsawon shekaru 55.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tanzania: MDD Ta Yi Kira Da A Yi Bincike Akan Daruruwan Mutanen Da Aka Kashe Sanadiyyar Rikcin Zabe November 12, 2025 Iran Ta Zama Memba A Kungiyar Tattara Bayanai Na Ilimomi Da Kere-kere Ta Duniya ( ISKO) November 12, 2025 Iran: Ta’addanci barazana ce ga dukkan yankin November 12, 2025 Araghchi: Matsalar Yammacin duniya ita ce ci gaban kimiyyar Iran ba makaman nukiliya ba November 12, 2025 Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon November 12, 2025 Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin November 12, 2025 Venezuela: Maduro Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tsaron Kasa Mai Cikakkiyar Kariya November 12, 2025 UNICEF: Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza November 12, 2025 Ministocin harkokin wajen kasashen yamma sun yi Allah wadai da ta’asar RSF a El Fasher Darfur November 11, 2025 Abdel-Aty: Diflomasiyya Ce Kawai Hanyar Da Maido Da Zaman Lafiya A Libya November 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci