Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan birnin Hudaidah na bakin ruwa a kasar Yemen a safiyar yau Talata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto tashoshin talabijin ta Almasirahtv ta kasar Yemen, da kuma Aljazeerah ta kasar Qatar  suna bada wannan labarin.

Sun kuma kara da cewa tun fara yaki a Gaza a shekara ta 2023 sojojin kasar Yemen suka hana jiragen kasuwanci na HKI wucewa ta babul Mandab na kasar Yemen wanda ya jawowa HKI asarori masu yawa, ya kuma gurgurta ayyukan tashoshin jiragen Ruwa na ummu Rashrash ko Ilat da kuma Haifa.

Sannan suna kaiwa hki hare-hare ne da makamai masu linzami kan tashar jiragen sama na Bengerion da kuma wuraren soje na kasar tun lokacin

Yemen na yin haka ne don goyon bayan  ga al-ummar Falasdinawa wadanda sojojin HKI suke ci gaba da yi masu kisan kare dangi tun lokaci har zuwa yanzu. Falasdinawa kimani 54000 hki ta kace ya zuwa yanzu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya

Ma’aikatar tsaron ta Amurka ta sanar da cewa za ta baza zaratan sojojin kasar na “Marines” akan titunan birnin Los Angeles domin fuskantar tashe-tashen hankulan da ake yi domin hana korar ‘yan ci-rani  ba bisa ka’ida ba.

Sanarwar ma’aikata tsaron kasar ta ce; Tuni na shirya sojojin na “Marines” 700 domin su yi aikli da rundunar “National Guards” wacce tuni tana kan titunan birnin bisa umarnin shugaba Donald Trump domin kama ‘yan hijira ba bisa ka’ida ba.

Ministan tsaron kasar ta Amurka  ya ce ; za a kai sojojin ne a cikin birnin saboda bayar da kariya ga muhimman gine-ginen gwamnatin tarayya da kuma dawo da doka da oda.

Shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya fada a jiya cewa, ba manufarsa ganin yakin basasa ya barke a Amurka ba, amma kuma ya yi wa masu tayar da kayar baya a cikin birnin Los Angeles barazanar dandana kudarsu saboda yadda suke cutar da rundunar kasa ( National Guards.)

A gefe daya gwamnan Jahar ta California Gavin Christopher dan jam’iyyar Democrat ya yi suka da kakkausar murya akan Shirin aikewa da zaratan sojojin na Amurka akan titunan birnin Los Angelos, yana mai cewa bai kamata a kai sojoji a cikin titunan Amurka ba.

Gwamnan ya kara da cewa; Aikewa da sojoji zuwa titunan California, wani kokari ne na Trump domin kara raba kan al’ummar kasar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za’ayi tattaunawa ta gaba tsakanin Iran da Amurka a ranar Lahadi a Oman
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kai Hare-Hare Kan Ayarin Motocin Agaji A Kan Hanyarsu Ta Kai Agajin Jin Kai 
  • Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe
  • Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya
  • Iran Ta Ce Wuraren Kai Farmaki A HKI Suna Hannu a Duka Sanda Ta Kawo hari Iran
  • Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe
  • Sojoji sun kashe kwamandan ’yan ta’adda a Yobe
  • Wasu Jiragen Ruwa Na  Ceto Da Jin Kai  Sun  Tashi Daga Tunisiya Zuwa Gabar Ruwan Gaza
  •  Rasha Ta Tarwatsa Mafi Yawancin Tankokin Yakin ” Abrams ” Na Amurka A Kasar Ukiraniya