Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4
Published: 11th, June 2025 GMT
Kamfanin Dakon Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da cewa za a dauke wutar lantarki a ilahirin jihohin yankin Arewa maso Gabas guda shida na tsawon kwana hudu.
A cikin wata wasika da ya aike wa kamfanonin rarraba wutar lantarki da ke kula da jihohin shida, TCN ya ce yayin da a wasu jihohin wutar za ta dauke gaba daya, wasu yankunan kuwa karancin wutar za a samu a tsakanin kwanakin.
Jihohin da lamarin zai shafa sun hada da Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Taraba da Yobe.
Kotu ta yi fatali da bukatar Akpabio, ta umarce shi ya biya Natasha N100,000 DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon LafiyaWasikar wacce ke dauke da sa hannun Jami’in Gudanarwa na Shiyyar Bauchi a TCN, Injiniya J.O Joseph, wacce aka aike wa daya daga cikin kamfanonin lantarkin, ta ce za a dauke wutar ne sakamakon saka babban layin dakon lantarki mai nauyin 330kV a karamar tashar lantarki da ke Bauchi.
Sanarwar ta kuma ce za a yi aikin gyaran ne daga tsakanin 10 zuwa 14 ga watan Yunin 2025.
Ta kara da cewa, “Yadda aikin zai kasance shi ne kamar haka; za a dauke wuta a layin Jos zuwa Gombe a tsawon wannan lokacin domin a samu damar saka manyan turakun dakon lantarki a sabuwar karamar tashar lantarki mai nauyin 330kV da ke Bauchi.
“Hakan na nufin ba za a sami wutar ba a garuruwan Damaturu, Molai, Yola da Jalingo, yayin da tashoshin lantarkin Gombe da Biu za su sami wutarsu ta cibiyar lantarki da ke Dadin Kowa, ita kuma karamar tashar lantarki da ke Baga Road za ta sami wutarta ne daga MEPP,” in ji sanarwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas Wutar Lantarki lantarki da ke wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
Aƙalla mutum huɗu ciki har da jaririn wata tara aka kashe a wani hari da aka kai ƙauyen Nkiendowro da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Mutanen da suka rasu sun haɗa da mata biyu da namiji ɗaya, wanda aka ce suna aikin jigilar kwashe tumatir daga ƙauyen zuwa kasuwar Farin-Gada da ke Jos lokacin da aka kai musu hari.
Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoWasu mutum biyu kuma sun jikkata a harin, wanda yanzu haka suna karɓar magani a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.
Shugaban tsaron al’ummar Miango, Josiah Zongo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin, yayin da waɗanda suka jikkata ke karɓar kulawa.
Rundunar ’yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba kan harin.
A wani lamari makamancin haka, an kai hari ƙauyen Murish da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a daren ranar Laraba, amma matasa da mazauna ƙauyen sun yi nasarar kare kansu daga maharan.
Wani matashi daga ƙauyen ya bayyana cewa maharan sun shigo suna harbi, amma mutanen ƙauyen sun kare kansu.
Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar Mwaghavul Development Association kuma shugaban sansanin ‘yan gudun hijira a Mangu, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu cikin lumana.
Ƙananan hukumomin Mangu da Bassa sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al’umma game da tsaro a Jihar Filato.