Jami’an tsaro a kasar Amurka sun cilla tear gas da albarusan roba kan masu zanga-zangar kin amincewa da shirin shugaba Trump na korar wasu Amurkawa wadanda ya kira bakin haure.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa, rikicin wanda aka fara tun kwanaki uku da suka gabata ya tashi ne bayan da jami’an shege da fice na Amurka suka kama wasu yan Latino da nufin korarsu daga kasar.

Sun kama mutane da dama a birnin Los Angeles a cikin rana kowa na gani. Gwamnan jihar Calfonia Gavin Newson ya rubuta a shafinsa na X kan cewa basu da wata matsa sai bayan da shugaba Trump ya aiko da ‘Sojojin Tarayya ko “National guard”, kuma wannan keta hurumin jihar ne, kuma shiga Trump tare da National Gurd shi ne rikita al-amura a jihar. Amma duk da haka zuwa safiyar yau Litinin kome ya lafa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI

Ministan leken asiri na kasar Iran ya ce asiran tsaron HKI da suka shiga hannun ma’aikatansa sun shafi makaman nukliya na HKI kuma sun nuna kwarewar da jami’an leken asirin kasar suke da shi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan bayanan zasu taimakawa sojojin JMI wajen sanin wuraren da zasu kai hare hare a duk lokacinda yake ya barke tsakanin Iran da haramtacciyar kasar, na makamai da kuma na yanar gizo.

Labarin ya kara da cewa  da jami’an ma’aikatar hukumar leken asiri suka yi kama daga daukar ma’aikatan da suka dace da yin hakan da dabar barun da suke yi amfani da su don kaiwa da bayan da suke bukata ya nuna irin koreawarsu a wannan aikin.

Sannan daga cikin muhimman bayanan da suka samu sun hada da na makaman nukliyar haramtacciyar kasar da kuma dangantakanta da Amurka da kuma kasashen turai rawar da wadan nan kasashe suka taka a karfafa HKI kan makamanta na kissan kaere dangi.

Ministan ya kammala da cewa bayanan da muka samu suna da muhimmanci haka ma hanyar da muka bi muka kai ga bayanan suna da muhimmanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai Wato Madleen
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai
  • Wagner ta kawo karshe kasantuwarta a Mali bayan fiye da shekaru uku
  • 2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
  • Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
  • Iran Ta Musanta Zargin Amurka Kan Cewa Kungiyoyi Masu Fada Ha HKI Suna Daukar Umurni Daga Wajenta Ne