Babban darektan hukumar IAEA ya zama tamkar wata yar tsana ce a hannun kasashen Yamma don dakile shirin nukiliyar Iran

An fara taron kwata-kwata na hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa a birnin Vienna, wanda ya samu halartar wakilan kasashe 35 mambobi hukumar

Bisa la’akari da rahoton da babban daraktan ya fitar game da sa ido da tabbatar da shirin nukiliyar Iran karkashin yarjejeniyar kare kai da kuma tsarin aiwatar da ayyukan hadin gwiwa ta (JCPOA) na daya daga cikin batutuwan da za a tattauna.

Babban darektan hukumar ta IAEA Rafa’el Grossi ya sanar a wani rahoto da ya fitar a makon da ya gabata cewa; Yawan sinadarin uranium da Iran ke da shi ya ninka har kashi 60 cikin dari. Kamar yadda ya yi zargin samuwar wata makamashin nukiliya da Iran ba ta bayyana ba a baya, yana mai nanata batutuwan da aka rufe a baya a cikin matsalar da ya shafi harkar soji (PMD) tun a shekara ta 2015.

A martanin da Iran ta mayar a hukumance ta nuna rashin amincewarta da rahoton, inda ta bayyana shi da cewa ya kaucewa aikin fasaha na hukumar IAEA da kuma Sanya batun siyasa da nuna son kai. A cikin wata sanarwa da hukumar ta IAEA ta Iran ta aikewa hukumar ta IAEA ta duniya, ta yi watsi da wadannan zarge-zargen, tare da tabbatar da cewa babu wasu ayyukan nukiliya da ba a bayyana ba a kasar Iran, kuma shirin nukiliyar kasar na da cikakken gaskiya kuma yana karkashin kulawar hukumar ta IAEA ta duniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hukumar ta IAEA

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jagorantar taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC) a ɗakin taro na Majalisar da ke Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

Kafin a fara taron, Shugaban Ƙasa ya rantsar da Farfesa Dakas James Dakas da Dakta Uchenna Eugene a matsayin Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki ta Ƙasa da Kwamishina.

Majalisar ta kuma dakatar da taron na minti ɗaya domin girmama marigayi Cif Audu Ogbe, wanda ya kasance memba a majalisar a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Shehu Shagari, haka kuma a ƙarƙashin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Cif Ogbe ya rasu a ranar Asabar, 9 ga watan Agusta, yana da shekaru 78.

 

Daga Bello Wakili

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Iran: Janar Hatami ya karbi bakuncin babban hafsan hafsoshin sojin Afirka ta kudu
  • Bankin Duniya zai kashe $300m domin inganta rayuwar ’yan gudun hijira a Arewacin Nijeriya
  • Yadda Kwastam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa
  • Yadda ɗan shekara 70 ya rasu a gobarar tankokin gas a Zariya
  • Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Gobe Talata