Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Babban Darektan Hukumar IAEA Saboda Yadda Yake Mika Wuya Ga Bakar Siyasa
Published: 10th, June 2025 GMT
Babban darektan hukumar IAEA ya zama tamkar wata yar tsana ce a hannun kasashen Yamma don dakile shirin nukiliyar Iran
An fara taron kwata-kwata na hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa a birnin Vienna, wanda ya samu halartar wakilan kasashe 35 mambobi hukumar
Bisa la’akari da rahoton da babban daraktan ya fitar game da sa ido da tabbatar da shirin nukiliyar Iran karkashin yarjejeniyar kare kai da kuma tsarin aiwatar da ayyukan hadin gwiwa ta (JCPOA) na daya daga cikin batutuwan da za a tattauna.
Babban darektan hukumar ta IAEA Rafa’el Grossi ya sanar a wani rahoto da ya fitar a makon da ya gabata cewa; Yawan sinadarin uranium da Iran ke da shi ya ninka har kashi 60 cikin dari. Kamar yadda ya yi zargin samuwar wata makamashin nukiliya da Iran ba ta bayyana ba a baya, yana mai nanata batutuwan da aka rufe a baya a cikin matsalar da ya shafi harkar soji (PMD) tun a shekara ta 2015.
A martanin da Iran ta mayar a hukumance ta nuna rashin amincewarta da rahoton, inda ta bayyana shi da cewa ya kaucewa aikin fasaha na hukumar IAEA da kuma Sanya batun siyasa da nuna son kai. A cikin wata sanarwa da hukumar ta IAEA ta Iran ta aikewa hukumar ta IAEA ta duniya, ta yi watsi da wadannan zarge-zargen, tare da tabbatar da cewa babu wasu ayyukan nukiliya da ba a bayyana ba a kasar Iran, kuma shirin nukiliyar kasar na da cikakken gaskiya kuma yana karkashin kulawar hukumar ta IAEA ta duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hukumar ta IAEA
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
Gwamnatin kasar Iran ta kai korafi a gaban hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD dangane da yakin da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar na tsawon kwanaki 12, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane fiye da 600.
Nasir Siraj wani jami’in ofishin jakadancin Iran a MDD ya mikawa kwamitionan hukumar Volker Türk a jiya Jumma’a .
Kafin haka dai ministan kiwon lafiya na kasar Iran ya bayyana cewa mutane 627 suka rasa rayukansu a yayinda wasu 4,870 suka ji rauni a yakin kwanaki 12 wanda wadannan kasashe biyu suka keta hurumin sararin samaniyar kasar. Yakin ya zo karshe ne bayan da HKI ta shelanta tsaida yaki ita kadai.
Korafin ya bayyan cewa abinda wadannan kasashe biyu suka yi ya sabawa dokokin kasa da kasa da dama, daga ciki har da dokar kasa da kasa ta kare hakkin bil’adama.