Ma’aunin Farashin Kayan Masarufi Na Watan Mayu A Kasar Sin Ya Ragu Da Kaso 0.1 Bisa Dari
Published: 9th, June 2025 GMT
Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta fitar a yau Litinin 9 ga wata sun nuna cewa, a watan Mayun bana, ma’aunin farashin kayayyakin masarufi, watau CPI na kasar, ya ragu da kaso 0.1 bisa dari, bisa na makamancin lokacin bara, kuma farashin makamashi ya zama babban dalilin da ya haifar da raguwar.
Duk da cewa ma’aunin CPI na watan Mayu ya ragu kadan, amma farashin kayayyaki a wasu bangarori ya canza, al’amarin da ya shaida rawar da manufofin ingiza harkokin saye da sayarwa ke takawa.
Kazalika, babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana a yau Litinin cewa, a farkon watanni biyar na shekarar da muke ciki, jimillar darajar hajojin da aka yi shige da ficensu a kasar Sin ta kai Yuan tiriliyan 17.94, adadin da ya karu da kaso 2.5 cikin dari, bisa na makamancin lokacin bara, wanda ya ci gaba da karuwa. Kana, jimillar cinikayyar da aka yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka ta kai matsayin koli a tarihi, inda jimillar hajojin da kasar Sin ta yi shige da ficensu a tsakaninta da kasashen Afirka, ta kai Yuan biliyan 963.21, adadin da ya karu da kaso 12.4 cikin dari, wanda ya dauki kaso 5.4 cikin dari na jimillar darajar hajojin da kasar Sin ta yi shige da ficensu. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: ya ragu da kaso a kasar Sin ta
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Rwanda Ta Fice Daga Cikin Kungiyar Tattalin Arziki Ta Tsakiyar Afirka
A daidai lokacin da kungiyar kasashen tsakiyar Afirka ta tattalin arziki ( ECCAS) take yin taro, kasar Rwanda ta sanar da ficewa daga cikinta.
Bayanin da gwamnatin kasar ta Rwanda ta fitar ya kunshi cewa; Kasar Rwanda tana nuna takaicinta akan yadda kasar DRC take amfani da kungiyar tattalin arziki ta tsakiyar Afirka a matsayin wani makamin a hannunta.”
Bayanin gwamnatin ta Rwanda ya kara da cewa: Yadda DRC take amfani da wannan kungiyar ya sake fitowa fili a yayin taron kungiyar karo na 26 a Malabo, ta yadda aka kau da kai akan hakkin Rwanda na shugabancin karba-karba,kamar yadda yake a cikin doka ta shida ta kundin kungiyar. Hakan kuma ya faru ne sanadiyyar shiftar DRC ga kungiyar.”
A yayin da aka shirya cewa a shekara mai zuwa kasar ta Rwanda za ta karfi shugabancin kungiyar, jami’an kasar DRC sun ce, ba za su sami halartar taron da za a yi a kasar ta Rwanda ba.
Kasashen biyu dai suna zaman tsami bisa zargin da Kinshasa take yi wa Kigali na cewa tana goyon bayan kungiyar ‘yan tawaye ta M23.
Yanzu dai kungiyar ta ECCAS tana da mamabobi 11 bayan ficewar kasar Rwanda. Kasashen su ne: Angola, Burundi, Cameroon, Afirka Ta Tsakiya,c, Congo, Gabon, Equatorial Guinea, Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, Rwanda, Sao Tome, sai tsibirin Principe da Chad.