Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta fitar a yau Litinin 9 ga wata sun nuna cewa, a watan Mayun bana, ma’aunin farashin kayayyakin masarufi, watau CPI na kasar, ya ragu da kaso 0.1 bisa dari, bisa na makamancin lokacin bara, kuma farashin makamashi ya zama babban dalilin da ya haifar da raguwar.

Kana, ma’aunin farashin sarrafa kaya na cikin gida, watau PPI shi ma ya ragu da kaso 3.3 bisa dari, bisa na makamancin lokacin bara, kuma adadin ya ragu da kaso 0.4 bisa dari, idan aka kwatanta da na watan Afrilun bana.

Duk da cewa ma’aunin CPI na watan Mayu ya ragu kadan, amma farashin kayayyaki a wasu bangarori ya canza, al’amarin da ya shaida rawar da manufofin ingiza harkokin saye da sayarwa ke takawa.

Kazalika, babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana a yau Litinin cewa, a farkon watanni biyar na shekarar da muke ciki, jimillar darajar hajojin da aka yi shige da ficensu a kasar Sin ta kai Yuan tiriliyan 17.94, adadin da ya karu da kaso 2.5 cikin dari, bisa na makamancin lokacin bara, wanda ya ci gaba da karuwa. Kana, jimillar cinikayyar da aka yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka ta kai matsayin koli a tarihi, inda jimillar hajojin da kasar Sin ta yi shige da ficensu a tsakaninta da kasashen Afirka, ta kai Yuan biliyan 963.21, adadin da ya karu da kaso 12.4 cikin dari, wanda ya dauki kaso 5.4 cikin dari na jimillar darajar hajojin da kasar Sin ta yi shige da ficensu. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ya ragu da kaso a kasar Sin ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara

Wata kotu a kasar Amurka ta yanke wa wasu ’yan Najeriya su biyar hukuncin daurin shekaru 159 bisa samun su da da laifin damfarar Amurkawa sama da 100.

Kotun dai ta sami mutanen ne da laifin damfarar kamfanoni da hukumomin gwamnatin kasar kudin da yawansu ya kai Dala miliyan 17, kwatwankwacin Naira biliyan 27 da miliyan 200.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sashen shari’a na kasar ya wallafa a shafinsa na intanet ranar Laraba, mai dauke da sa hannun mai rikon mukamin Babban Lauyan gwamnati na gundumar gabashin Texas, Ray Combs.

’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara

Sanarwar ta ce mutanen da aka yanke wa hukuncin sun hada da Damilola Kumapayi, Sandra Iribhogbe, Edgal Iribhogbe, Chidindu Okeke and Chiagoziem Okeke, kuma mambobi ne a wani gungun ’yan damfara na kasa da kasa.

Lauyan ya ce ’yan damfarar sun fara harkallar ne tun a shekara ta 2017, inda suke hakon tsofaffi da kuma masu rangwamen gata ta hanyar kirkiro dabaru daban-daban na karbar kudi daga wajensu, wasu lokutan ma ilahirin abin da suka tara a rayuwarsu.

“Da zarar sun karbi kudade daga mutane ta hanyar damfarar, sai su tuttura su ta hanyar asusun ajiya a bankuna da dama da kuma abokan harkallarsu da ’yan kasuwa da ke kasashe a nahiyoyin Afirka da Asiya,” in ji lauyan na gwamnatin Amurka.

Sanarwar ta ce bayan kama su, an gurfaran da su a gaban kotu kan laifukan da suka hada da hadin baki, zambar kudade da kuma damfara, wadanda dukkansu suka amsa aikatawa.

A cewar sanarwar, hakan ce ta sa alkalin kotun, Mai Shari’a Amos Mazzant, ya yanke musu hukuncin daurin shekaru daban-daban a kurkuku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala
  • Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev