Iran: Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Tace Zata Maida Martani Kan Hukumar IAEA
Published: 11th, June 2025 GMT
Iran ta bada sanarwan cewa ta sharia matakan da zata dauka kan hukuma IAEA mau kula da makamashin nukliya ta duniya idan ta samar da kudurin yin allawadai ko kuma rashin bada ahadin kai ga hukumar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’ik Baghae yana fadara haka a jiya Talata .
Baghae yayi allawadai da rahoton da Daraktan hukumar IAEA Rafael Grossi ya bayar dangane da shirin Nukliyar kasar kafin taron gwamnonin hukumar.
Yace wannan a fili ya nuna cewa hukumar AIEA tana aiki ne don dadadwa makiyan JMI wato Amurka da HKI. Grossi a rahotonsa ya bayyana cewa Iran ta ki ta bayyana ayyukan nukliyan da take yi a wurare uku a cikin kasar. Da kuma yadda ta tache makamancin Uranium har zuwa kashi 60%.
Ya kammala da cewa Iran ta dade tana shakkan ayyukan shugaban hukumar Makamashin nukliya ta IAEA, amma a cikin wasikun sirri da suka samu ta hanyar leken asiri sun tabbatar da abinda muke shakka.
Mohammad Eslamu daractan hukumar makamashin Nukliya ta kasar ya yi tir da rahoron grossi wanda a fili yana taimakawa maikan JMI a dai dai lokacinda yakamata a zama dan ba ruwammu ya daina shiga harkokin siyasa. Banda haka rahoton nasa bai da kima ga kwarraru wadanda suka san ayyukan makamashin nukliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukliya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na kira ga Amurka, da ta gaggauta dakatar da shuka kiyayya, da haifar da tashin hankali, da rura wutar gaba a tekun kudancin kasar Sin, kana ta kyale a dawo da yanayin zaman lafiya da daidaito a yankin. Lin Jian, ya bayyana hakan ne yau Litinin, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, lokacin da aka yi masa tambaya kan batun.
Wasu rahotanni daga kafofin watsa labarai sun bayyana cewa, a baya bayan nan, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ya fitar da sanarwa dake cewa Amurka na goyon bayan kasar Philippines, game da watsi da ta yi da tsare-tsaren kasar Sin na kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin Huangyan Dao.
Lin ya ce “Mun gabatar da kakkarfan korafi a yau, dangane da kuskuren da Amurka ta tafka. Tsibirin Huangyan Dao yankin kasar Sin ne tun fil azal”, kuma kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin na karkashin ikon mulkin kai na Sin, wanda hakan ke nufin yana bisa turba, ya dace da doka, bai kuma cancanci suka ba. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp