NAFDAC Ta Kaddamar Da Sabbin Shirye-Shiryen Yaki Da Jaribun Magunguna
Published: 27th, February 2025 GMT
Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta sake jaddada aniyar ta na dakile yaduwar magungunan jabun a fadin kasar nan.
Darakta Janar na Hukumar Farfesa Mojisola Christianah Adeyeye ta bayyana hakan a yayin bikin bude taron wayar da kan jama’a na kwanaki biyu da aka gudanar a Kano.
Farfesa Mojisola Christianah wacce Darakta Pharmacist, Pharmacist Bitrus Fraden ta wakilta ta ce NAFDAC ta bullo da wasu sabbin tsare-tsare guda uku da nufin inganta hanyoyin magance yaduwar magungunan jabu a kasar.
Babban Daraktan ya jaddada bukatar masu ruwa da tsaki su tallafa wa wadannan tsare-tsare, da nufin tabbatar da samar da ingantattun kayayyakin kiwon lafiya, masu inganci ga ‘yan Nijeriya.
Ta ce Najeriya ita ce kasa ta farko a Afirka da ta fara amfani da wannan fasahar, wanda ke baiwa masu ruwa da tsaki damar ganowa da kuma watsi da kayayyakin da basu da inganci.
“Dokar hukumar kula da lafiyar yara ta NAFDAC mai lamba 2024 wata ka’ida ce ta musamman da ke magance bukatu na musamman na yara. Wannan ka’ida ta ginu ne a kan tsarin rijistar da ake da shi, yana ba da karin kariya don tabbatar da tsaro da ingancin kayayyakin kiwon lafiya ga yara.”
A nata bangaren wata mataimakiyar darakta Regina Garba ta ce makasudin taron shi ne wayar da kan masu ruwa da tsaki kan hadin gwiwa ta wannan fanni.
Ko’odinetan NAFDAC na shiyyar Arewa maso Yamma Mista Fadi Nantim Mullah ya ce makasudin gudanar da taron bitar a shiyyar ya kasance ne saboda yawaitar masu sana’ar magunguna musamman a Kano.
Abdullahi Jalaluddeen Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
A cewarsa, tuni aka shirya wuraren kwana da abinci ga maniyyatan a kasar Saudiyya.
Abdulkadir ya tabbatar da cewa, ana shirye-shirye, inda za a yi alluran rigakafi a ranar 28 ga Afrilu, za a raba tufafi a 30 ga Afrilu, sannan kuma za a raba jakunkuna a ranar 1 ga Mayu.
Ya kara da cewa maniyyatan da suka biya sama da Naira miliyan 8.4 na kudin aikin Hajji, za a biya su bayan sun dawo daga Saudiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp