NAFDAC Ta Kaddamar Da Sabbin Shirye-Shiryen Yaki Da Jaribun Magunguna
Published: 27th, February 2025 GMT
Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta sake jaddada aniyar ta na dakile yaduwar magungunan jabun a fadin kasar nan.
Darakta Janar na Hukumar Farfesa Mojisola Christianah Adeyeye ta bayyana hakan a yayin bikin bude taron wayar da kan jama’a na kwanaki biyu da aka gudanar a Kano.
Farfesa Mojisola Christianah wacce Darakta Pharmacist, Pharmacist Bitrus Fraden ta wakilta ta ce NAFDAC ta bullo da wasu sabbin tsare-tsare guda uku da nufin inganta hanyoyin magance yaduwar magungunan jabu a kasar.
Babban Daraktan ya jaddada bukatar masu ruwa da tsaki su tallafa wa wadannan tsare-tsare, da nufin tabbatar da samar da ingantattun kayayyakin kiwon lafiya, masu inganci ga ‘yan Nijeriya.
Ta ce Najeriya ita ce kasa ta farko a Afirka da ta fara amfani da wannan fasahar, wanda ke baiwa masu ruwa da tsaki damar ganowa da kuma watsi da kayayyakin da basu da inganci.
“Dokar hukumar kula da lafiyar yara ta NAFDAC mai lamba 2024 wata ka’ida ce ta musamman da ke magance bukatu na musamman na yara. Wannan ka’ida ta ginu ne a kan tsarin rijistar da ake da shi, yana ba da karin kariya don tabbatar da tsaro da ingancin kayayyakin kiwon lafiya ga yara.”
A nata bangaren wata mataimakiyar darakta Regina Garba ta ce makasudin taron shi ne wayar da kan masu ruwa da tsaki kan hadin gwiwa ta wannan fanni.
Ko’odinetan NAFDAC na shiyyar Arewa maso Yamma Mista Fadi Nantim Mullah ya ce makasudin gudanar da taron bitar a shiyyar ya kasance ne saboda yawaitar masu sana’ar magunguna musamman a Kano.
Abdullahi Jalaluddeen Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.
Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a ChinaUwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.
Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.
Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.