Ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin, ta sanar a jiya Asabar cewa bisa gayyatar da gwamnatin Birtaniya ta yi masa, memba a hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, kana mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng, zai ziyarci Birtaniya tun daga yau Lahadi har zuwa Juma’a 13 ga watan nan na Yuni.

 

Ana sa ran yayin ziyarar tasa a Birtaniya, He Lifeng zai halarci taron farko na tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka.

(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baghae ya zargin gwamnatin Amurka da yin ba daidai ba saboda karin takunkuman tattalin arziki wanda ta dorawa kasar, wanda kuma yake nuna irin kiyayyar da takewa mutanen kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Esmael Baghae yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa bayan da hukumar baitul malin Amurka ta bayyana sunayen mutane 10 wadanda ta dorawa takunkuman tattalin arziki da kuma kamfanoni 27 mafi yawansu a hadaddiyar daulolin larabawa wato UAE.

Labarin ya kara da cewa wadan nan mutane suna taimakawa Iran a ayyukan Banki da jigilar manfetur a madadin Iraniyawa. Baghae ya bayyana wannan labarin a kan kariya kuma mummunan siyasar Amurka ce ga JMI.

Yace bayan haka wadan nan takunkuman basa bisa ka’idar doka kuma manufa it ace takurawa mutanen kasar Iran.

Sannan ya kammala da cewa wadan nan matakan zasu kara karfafa dauriyan mutanen kasar Iran ne kawai. Inji Baghe.

Sannan abin mamaki shi ne wadannan takunkuman suna zuwa ne a dai-dai lokacinda kasashen biyu suke tattaunawa kan shirin makamashin Nukliya na kasar. Wanda ya nuna cewa Amurka bata nufin alkhairi a tattaunawar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran
  • Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
  • Amurka Ta Sake Dorawa Iran Karin Takunkuman Tattalin Arziki Duk Tare Da Tattaunawa A Tsakaninsu
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
  • Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
  • Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
  • Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho