Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000
Published: 8th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu, ya bai wa alhazan jihar su 3,200 kyautar Riyal 1,000 na Saudiyya (kimanin Naira 450,000) a matsayin barka da sallah.
Gwamnan, ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya kai wa alhazan ziyara a Minna.
Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a JigawaYa taya su murna bisa kammala aikin Hajji lafiya, inda ya ce wannan kyauta ce domin tallafa musu kafin su dawo gida Najeriya.
Gwamna Aliyu, ya yaba da yadda alhazan suka kiyaye doka da oda a ƙasa mai tsarki, inda ya ce sun wakilci Jihar Sakkwato cikin ƙwarewa da girmamawa.
Ya kuma gode musu bisa ladabi da haƙuri da suka nuna yayin gudanar da ibadar Hajji.
Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kula da jin daɗin al’ummar jihar, musamman mahajjata.
Haka kuma, ya jinjina wa ƙoƙarin Amirul Hajj na jihar, Alhaji Ummarun Kwabo, da kuma Hukumar Alhazai ta jihar bisa jajircewarsu wajen tsara Hajjin bana cikin nasara.
Gwamnan, ya kuma roƙi alhazan da su ƙara yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da tsaro a Najeriya.
Ya ce duk da irin ƙoƙarin da ake yi wajen magance matsalolin tsaro, addu’a ita ce mafi tasiri wajen kawo ƙarshen matsalar da ke hana ci gaban ƙasa.
A yayin ziyarar, Gwamna Aliyu, ya jajanta wa akhazai daga ƙananan hukumomin Gudu da Shagari bisa rasuwar Hajiya Hadiza da Bala Jangebe a lokacin aikin Hajji.
Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta musu kuma Ya bai wa iyalansu haƙuri rashinsu.
A nasa jawabin, Amirul Hajji, Alhaji Ummarun Kwabo, ya gode wa gwamnan bisa goyon bayansa, wanda ya ce shi ne ya taimaka wajen samun nasarar aikin Hajjin bana.
Ya ƙara da cewa dukkanin kwamitocin da aka kafa sun yi aiki tuƙuru don ganin komai ya tafi lafiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barka Da Sallah Gwamna Ahmed kyauta Sakkwato Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya
Jimillar fursunoni: 80,879
Adadin cibiyoyin gyaran hali: 256
Kashi na rijista da aka kammala: 74%
Umar ya jaddada cewa sauran fursunonin da ba a yi wa rijistar ba za a cigaba da yi musu, kuma an kafa duk wasu hanyoyi da za su tabbatar da nasarar kammala aikin cikin sauki.
Hukumar ta bayyana wannan aikin a matsayin wani muhimmin mataki na inganta tsarin dijital, da sake gyaran rayuwa, da shigar da fursunoni cikin tsarin ƙasa.
Ya kuma buƙaci kafafen yaɗa labarai da su tabbatar da sahihancin bayanansu daga hukumomin da suka dace kafin wallafawa domin kaucewa yaɗa bayanan da za su iya dagula fahimtar jama’a ko rage ƙwarin gwuiwar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp