Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000
Published: 8th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu, ya bai wa alhazan jihar su 3,200 kyautar Riyal 1,000 na Saudiyya (kimanin Naira 450,000) a matsayin barka da sallah.
Gwamnan, ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya kai wa alhazan ziyara a Minna.
Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a JigawaYa taya su murna bisa kammala aikin Hajji lafiya, inda ya ce wannan kyauta ce domin tallafa musu kafin su dawo gida Najeriya.
Gwamna Aliyu, ya yaba da yadda alhazan suka kiyaye doka da oda a ƙasa mai tsarki, inda ya ce sun wakilci Jihar Sakkwato cikin ƙwarewa da girmamawa.
Ya kuma gode musu bisa ladabi da haƙuri da suka nuna yayin gudanar da ibadar Hajji.
Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kula da jin daɗin al’ummar jihar, musamman mahajjata.
Haka kuma, ya jinjina wa ƙoƙarin Amirul Hajj na jihar, Alhaji Ummarun Kwabo, da kuma Hukumar Alhazai ta jihar bisa jajircewarsu wajen tsara Hajjin bana cikin nasara.
Gwamnan, ya kuma roƙi alhazan da su ƙara yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da tsaro a Najeriya.
Ya ce duk da irin ƙoƙarin da ake yi wajen magance matsalolin tsaro, addu’a ita ce mafi tasiri wajen kawo ƙarshen matsalar da ke hana ci gaban ƙasa.
A yayin ziyarar, Gwamna Aliyu, ya jajanta wa akhazai daga ƙananan hukumomin Gudu da Shagari bisa rasuwar Hajiya Hadiza da Bala Jangebe a lokacin aikin Hajji.
Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta musu kuma Ya bai wa iyalansu haƙuri rashinsu.
A nasa jawabin, Amirul Hajji, Alhaji Ummarun Kwabo, ya gode wa gwamnan bisa goyon bayansa, wanda ya ce shi ne ya taimaka wajen samun nasarar aikin Hajjin bana.
Ya ƙara da cewa dukkanin kwamitocin da aka kafa sun yi aiki tuƙuru don ganin komai ya tafi lafiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barka Da Sallah Gwamna Ahmed kyauta Sakkwato Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
’Yan sanda a jihar Legas sun kama wani tsohon fursuna tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a jerin laifukan fashi da yankan aljihu a jihar kwana biyar da fitowa daga kurkuku.
Tsohon fursunan mai shekaru 25 da haihuwa, Segun Kolawole, an kama shi ne bayan kwana biyar da aka sako shi daga cibiyar gyaran hali ta Kirikiri, a jihar Legas.
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano SpalletiSauran wadanda aka kama tare da shi sun haɗa da Sodiq Isa mai shekaru 27 da Adekanmbi Ganiu mai shekaru 21.
Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne bisa laifukan yankan aljihun mutane da sauran laifukan sata a sassa daban-daban na jihar.
Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke Kolawole, inda ta ce an kama shi da misalin ƙarfe 8 na safiyar Talata a kasuwar Oshodi, bayan jami’ai sun lura da motsinsa da ya zama abin zargi.
Adebisi ta ce an same shi da tsabar kuɗi ₦80,000 da wayar Infinix Note 40 Pro, waɗanda aka gano daga wani fashi da ya aikata a Opebi, inda ake zargin ya saci ₦200,000 da wayar daga hannun wani ɗan kasuwa da ke barci.
“Bincike ya ƙara tabbatar da cewa ya riga ya sayi sabbin kaya da takalma da wani ɓangare na kuɗin da ya sata, waɗanda suma aka kwato su daga hannunsa,” in ji ta.
Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar Juma’a, jami’an RRS sun kama Sodiq Isa da Adekanmbi Ganiu bisa zargin yunkurin satar wayoyin hannu daga hannun fasinjoji a sassa daban-daban na Legas.