Aminiya:
2025-07-24@04:19:15 GMT

Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000

Published: 8th, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu, ya bai wa alhazan jihar su 3,200 kyautar Riyal 1,000 na Saudiyya (kimanin Naira 450,000) a matsayin barka da sallah.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya kai wa alhazan ziyara a Minna.

Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa

Ya taya su murna bisa kammala aikin Hajji lafiya, inda ya ce wannan kyauta ce domin tallafa musu kafin su dawo gida Najeriya.

Gwamna Aliyu, ya yaba da yadda alhazan suka kiyaye doka da oda a ƙasa mai tsarki, inda ya ce sun wakilci Jihar Sakkwato cikin ƙwarewa da girmamawa.

Ya kuma gode musu bisa ladabi da haƙuri da suka nuna yayin gudanar da ibadar Hajji.

Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kula da jin daɗin al’ummar jihar, musamman mahajjata.

Haka kuma, ya jinjina wa ƙoƙarin Amirul Hajj na jihar, Alhaji Ummarun Kwabo, da kuma Hukumar Alhazai ta jihar bisa jajircewarsu wajen tsara Hajjin bana cikin nasara.

Gwamnan, ya kuma roƙi alhazan da su ƙara yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da tsaro a Najeriya.

Ya ce duk da irin ƙoƙarin da ake yi wajen magance matsalolin tsaro, addu’a ita ce mafi tasiri wajen kawo ƙarshen matsalar da ke hana ci gaban ƙasa.

A yayin ziyarar, Gwamna Aliyu, ya jajanta wa akhazai daga ƙananan hukumomin Gudu da Shagari bisa rasuwar Hajiya Hadiza da Bala Jangebe a lokacin aikin Hajji.

Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta musu kuma Ya bai wa iyalansu haƙuri rashinsu.

A nasa jawabin, Amirul Hajji, Alhaji Ummarun Kwabo, ya gode wa gwamnan bisa goyon bayansa, wanda ya ce shi ne ya taimaka wajen samun nasarar aikin Hajjin bana.

Ya ƙara da cewa dukkanin kwamitocin da aka kafa sun yi aiki tuƙuru don ganin komai ya tafi lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barka Da Sallah Gwamna Ahmed kyauta Sakkwato Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

Alkaluma da aka fitar a hukumance sun nuna cewa, kasar Sin ta samar da sabbin guraben aikin yi miliyan 6.95 a rabin farko na bana, inda ta cimma kaso 58 bisa dari na burinta na shekara.

Kakakin ma’aikatar kula da ma’aikata da walwalar al’umma ta kasar Sin Cui Pengcheng ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai a yau Talata, inda ya ce a watan Yuni, yawan wadanda ba su da aiki a birane ya tsaya kan kaso 5 bisa dari, watau bai sauya ba daga yadda ya kasance shekara 1 da ya wuce.

Kasar Sin na da burin adadin marasa aikin yi ya tsaya kan kaso 5.5 a bana, tare da burin samar da guraben aikin yi sama da miliyan 12. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Asibitin ATBUTH za ta fara gwajin rigakafin zazzaɓin Lassa
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar