Aminiya:
2025-11-03@12:37:03 GMT

Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya 

Published: 8th, June 2025 GMT

Ƙasar Zambiya ta ayyana zaman makoki na kwanaki bakwai don girmama tsohon shugaban ƙasar, Edgar Lungu, wanda ya rasu a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni, 2025, a ƙasar Afirka ta Kudu.

Ya rasu yana da shekaru 68.

Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce

Lungu ya shugabanci Zambiya daga watan Janairun shekarar 2015 har zuwa watan Agustan 2021, lokacin da ya sha kaye a hannun shugaban ƙasa mai ci yanzu, Hakainde Hichilema.

Gwamnati ta sanar da cewa daga ranar 8 zuwa 14 ga wata Yuni, duk tutocin ƙasar za su kasance a ƙasa, sannan kuma an dakatar da duk wasu tarukan nishaɗi a wannan lokacin domin nuna alhini da mutunta tsohon shugaban.

Sakataren majalisar ministoci, Patrick Kangwa, ya bayyana cewa Shugaba Hichilema ya amince da yi wa Lungu jana’izar ƙasa.

An shirya dawowar gawarsa zuwa Zambiya a ranar Laraba mai zuwa.

Gwamnatin ƙasar ta ce Belvedere Lodge da ke babban birnin Lusaka ita ce cibiyar da aka ware don gudanar da makokin.

Kafin rasuwarsa, Lungu na ƙarƙashin kulawar likita a wani asibiti da ke Pretoria, Afirka ta Kudu.

Jam’iyyarsa ta Patriotic Front (PF) ta ce ya sha fama da wata cuta mai suna “achalasia” wata matsala ce da ke hana abinci wucewa a maƙogwaro yadda ya kamata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Edgar Lungu rasuwa Zambiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.

Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.

Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.

Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).

Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.

Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.

Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”

Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.

Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.

Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.

Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.

A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.

Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 
  • Tsagin Damagum da Anyanwu sun shirya mamaye hedikwatar PDP a yau
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki