Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya
Published: 8th, June 2025 GMT
Ƙasar Zambiya ta ayyana zaman makoki na kwanaki bakwai don girmama tsohon shugaban ƙasar, Edgar Lungu, wanda ya rasu a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni, 2025, a ƙasar Afirka ta Kudu.
Ya rasu yana da shekaru 68.
Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuceLungu ya shugabanci Zambiya daga watan Janairun shekarar 2015 har zuwa watan Agustan 2021, lokacin da ya sha kaye a hannun shugaban ƙasa mai ci yanzu, Hakainde Hichilema.
Gwamnati ta sanar da cewa daga ranar 8 zuwa 14 ga wata Yuni, duk tutocin ƙasar za su kasance a ƙasa, sannan kuma an dakatar da duk wasu tarukan nishaɗi a wannan lokacin domin nuna alhini da mutunta tsohon shugaban.
Sakataren majalisar ministoci, Patrick Kangwa, ya bayyana cewa Shugaba Hichilema ya amince da yi wa Lungu jana’izar ƙasa.
An shirya dawowar gawarsa zuwa Zambiya a ranar Laraba mai zuwa.
Gwamnatin ƙasar ta ce Belvedere Lodge da ke babban birnin Lusaka ita ce cibiyar da aka ware don gudanar da makokin.
Kafin rasuwarsa, Lungu na ƙarƙashin kulawar likita a wani asibiti da ke Pretoria, Afirka ta Kudu.
Jam’iyyarsa ta Patriotic Front (PF) ta ce ya sha fama da wata cuta mai suna “achalasia” wata matsala ce da ke hana abinci wucewa a maƙogwaro yadda ya kamata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Edgar Lungu rasuwa Zambiya
এছাড়াও পড়ুন:
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
A cewarsa, damar kauwancin da ake samu daga fannin an same ta ne, saboda yadda Matatar ta Dangote, ke sarrafa danyen Mai wanda kuma ‘ya’yan kungiyar, ke son ganin sun amafana da hakan daga Matatar ta Dangote.
Madugu ya ci gaba da cewa, wasu daga cikin bangarorin da kungiyar za ta amfana daga Matatar ya ce, sun hada da, Man da ake sarrafawa daga danye Mai, Man Dizil, Kalanzir, Man Jirgin Sama da kuma Iskar Gas, samfarin LPG.
Sauran ya ce, sun ne, sanadaran naphtha, bitumen, ethylene, propylene da sauransu.
Kazalika, ya kuma jinjinawa Shugaban rukunin Matatar Man ta Dangote, Aliko Dangote, bisa namijin kokarin da ya yi, na kafa Matatar Man a kasar nan.
Tawagar ta kungiyar MAN, ta kuma karrama Dangote da mai bai wa shugaban kasa shawara ta musamman a bangaren hudda da jama’a da kuma jagorar aikin rukunin Matatar Madam Fatima Wali-Abdurrahman da babbar lambar yabo.
A kwanan baya ne, Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya amince da sanya kaso 15 a cikin dari kan Man Fetur da Man Dizil da ake shigowa da su cikin kasar daga ketare, inda danganta tsarin, a matsayin matakin sarrafa Mai a cikin kasar da kuma rage yin dogaro kan makamashin da ake shigowa da shi, daga waje.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA