Aminiya:
2025-06-19@18:27:25 GMT

Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya 

Published: 8th, June 2025 GMT

Ƙasar Zambiya ta ayyana zaman makoki na kwanaki bakwai don girmama tsohon shugaban ƙasar, Edgar Lungu, wanda ya rasu a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni, 2025, a ƙasar Afirka ta Kudu.

Ya rasu yana da shekaru 68.

Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce

Lungu ya shugabanci Zambiya daga watan Janairun shekarar 2015 har zuwa watan Agustan 2021, lokacin da ya sha kaye a hannun shugaban ƙasa mai ci yanzu, Hakainde Hichilema.

Gwamnati ta sanar da cewa daga ranar 8 zuwa 14 ga wata Yuni, duk tutocin ƙasar za su kasance a ƙasa, sannan kuma an dakatar da duk wasu tarukan nishaɗi a wannan lokacin domin nuna alhini da mutunta tsohon shugaban.

Sakataren majalisar ministoci, Patrick Kangwa, ya bayyana cewa Shugaba Hichilema ya amince da yi wa Lungu jana’izar ƙasa.

An shirya dawowar gawarsa zuwa Zambiya a ranar Laraba mai zuwa.

Gwamnatin ƙasar ta ce Belvedere Lodge da ke babban birnin Lusaka ita ce cibiyar da aka ware don gudanar da makokin.

Kafin rasuwarsa, Lungu na ƙarƙashin kulawar likita a wani asibiti da ke Pretoria, Afirka ta Kudu.

Jam’iyyarsa ta Patriotic Front (PF) ta ce ya sha fama da wata cuta mai suna “achalasia” wata matsala ce da ke hana abinci wucewa a maƙogwaro yadda ya kamata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Edgar Lungu rasuwa Zambiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra

Wani yaro mai kimanin shekaru goma a duniya ya harbe mahaifinsa wanda jami’in ɗan sanda ne mai mukamin sufeto a Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Nijeriya.

Haka kuma, wakilinmu ya ruwaito cewa yaron ya harbi wani yayansa da bindigar mahaifin nasa ta aiki kirar AK-47.

Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Anambra, Tochukwu Ikenga ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Kakakin ya ce an gaggauta kai jamin asibiti domin a ceto rayuwarsa amma likitoci suka tabbatar da cewa rai ya riga ya yi halinsa.

Sanarwar ta ce “a ranar Lahadi 15 ga watan Yuni, dan gidan wani jami’in dan sanda mai kimanin shekara goma da haihuwa ya harbe mahaifinsa har lahira ya kuma jiwa yayan sa mummunan rauni.

“Abin bakin ciki muna sanar da ku mutuwar jami’inmu mai mukamin sufeto, Okolie Amechi, bisa harbe shi da dansa ya yi a gidansa.

“Wannan ba karamin abin takaici ba ne da kaddara,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra