Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba
Published: 7th, June 2025 GMT
“Gidauniyarmu ta farko da aka kafa a shekarar 1952, ta tallafa wa masu fasaha daban-daban na Afirka, ta hanyar ba su damar shiga kasuwannin duniya. Gidauniyar Egbuagu, wadda aka kaddamar a yau; za ta mayar da hankali ne wajen kula da ayyukan shari’a, domin taimaka wa ‘yan Nijeriyan da ake tsare da su ba bisa ka’ida ba,” in ji shi.
“Babban bangaren da za mu bai wa fifiko shi ne, na matasan fursunoni, masu basirar kirkire-kirkire. Muna so mu taimaka musu su yi amfani da kwarewarsu, domin samun damar rike kawunansu ko da kuwa a gidajen yarin ne. Kazalika, bincikenmu zai mayar da hankali kan shekaru da kuma yanayin daurin da aka yi musu.”
Dangane da batun hadin gwiwa kuwa, Egbuagu ya kara da cewa; “Mun shirya yin aiki tare da kungiyoyin lauyoyi, ciki har da masu yin aiki kyauta. Tuni dai, wasu daga cikin kamfanonin lauyoyi da dama suka yi alkawarin taimaka mana, yayin da wasu lauyoyin kuma suka sha alwashin yin aiki da mu kyauta, a wasu lokutan kuma za mu biya su; idan akwai bukatar hakan.
Ya kara da cewa, ‘yan Nijeriya su yi tsammanin fara cikakken wannan aiki na gidauniya nan da watan Yunin 2025.
“A yanzu haka, muna kokarin kammala yarjejeniya tare da abokan aikinmu tare kuma da gabatar da kawunanmu ga gidajen fursunonin da ayyana abubuwan da muke son aiwatarwa. Mafi yawan wadannan fursunoni, ba su da ko da fayel, don haka; a cikin tsarikan da muke da su, za mu samar musu da fayal-fayal tare kuma da rubuta dalilan da yasa bai kamata su ci gaba da kasancewa a wadannan wurare ba.
“Wannan aiki, ko shakka babu zai dauki kimanin kwana 90, bayan haka; za mu fara shiga tsakani tare kuma da sanar da kamfanoni masu zaman kansu.”
Wata babbar lauya, mai suna Zikora Okwor-Wewan, wadda ita ma ta halacci kaddamarwar, ta bayyana farin cikinta game da wannan shiri, “Na yi aiki da fursunonin da ke jiran shari’a da kuma wadanda aka daure a gidajen yari ba bisa ka’ida ba. Lokacin da na ji batun wannan gidauniya, na yi matukar murna tare da yanke shawarar kasancewa tare da ita. Haka zalika, taimakawa wajen ‘yantar da fursunoni kimanin 1,000, na daya daga cikin ayyukan da nake so tare kuma da sha’awar yi”, in ji ta.
Har ila yau, ya sake nanata wannan kididdiga: “Nijeriya na da fursunoni kimanin 80,000, amma kusan kashi 70 cikin 100, har yanzu suna nan suna jiran shari’a. Kazalika, kusan kimanin 26,000 daga cikinsu, kananan yara ne, wadanda ko dai wadanda aka kama ko kuma wadanda aka haifa a can. Wasunsu ma, ba su da ko da shaidar takardun haihuwa, wasu kuma sun makale ne kawai a cikin tsarin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tare kuma da
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Cutar amosanin jini wacce aka fi sani da cutar sikila na cigaba da barazana ga rayukan masu dauke da ita.
Wannan cuta na saka masu ita da ‘yan uwan su cikin halin ha’ula’i, a wasu lokutan ma tana haifar da rasa rayukan wasu dake dauke da ita.
Rahotannin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) sun nuna cewa, kusan yara 300,000 ne ake haifa da cutar Sikila a duk shekara a fadin duniya, inda yankin Kudu da Sahara a Afirka ke dauke da kashi 75% na wannan yawan.
A Najeriya kadai, ana kiyasta cewa fiye da yara 150,000 ake haifa da cutar Sikila a kowace shekara — hakan ya sa Najeriya ke da mafi yawan masu fama da cutar Sikila a duniya.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan cutar amosanin jini don gano yadda masu fama da ita ke ji a rayuwar su.
Domin sauke shirin, latsa nan