HausaTv:
2025-06-15@10:26:24 GMT

Isra’ila Ta Saki Fursunonin Falasdinawa Da Dama

Published: 27th, February 2025 GMT

Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa da dama a daidai lokacin da kungiyar Hamas ta mika gawarwakin ‘yan Isra’ila hudu ga kungiyar agaji ta Red Cross.

Fursunonin sun isa birnin Ramallah da ke gabar yammacin kogin Jordan ne a kan motocin kungiyar agaji ta Red Cross bayan sun tashi daga gidan yarin Ofer da ke yankin da aka mamaye.

Musayar ta karkare kashi na farko na musayar da aka faro tsakanin bangarorin biyu, wanda ke gudana a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka fara aiwatarwa a watan da ya gabata da fatan kawo karshen yakin kisan kare dangi da gwamnatin Isra’ila ta yi wa Gaza na tsawon watanni 15.

Falasdinawan da aka sako na cikin fursunoni sama da 600, wadanda gwamnatin kasar ta ce za ta saki a matakin farko.

Baki daya, a matakin farko kungiyar Hamas ta mika ‘yan Isra’ila 33 da ta yi garkuwa dasu da suka hada da gawarwaki takwas, domin musayar fursunonin Falasdinawa kusan 2,000.

Tun ranar Asabar data gabata ce ya kamata gwamnatin Isra’ila ta mika fusunonin Falasdinawan su 206, saidai Isra’ila ta jinkirta sakin fursunonin bayan da kungiyar Hamas ta mika wasu ‘yan Isra’ila shida daga Gaza, tana mai cewa Hamas na wulakanta ‘yan kasarta a yayin bikin mika su.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)

Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.

“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.

Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.

A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.

Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini