Kotu ta yi fatali da bukatar Akpabio, ta umarce shi ya biya Natasha N100,000
Published: 11th, June 2025 GMT
Kotun Daukaka Kara da ke Abuja ta yi fatali da bukatun Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio kan dakatacciyar Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, sannan ta ci shi tarar Naira 100,000.
Kotun, wacce ke karkashin jagorancin Mai Shari’a Hamman Barka dai ta yi watsi da bukatun ne kan karar da aka shigar ranar 21 ga watan Mayun 2025, bayan neman bukatar janye karar da aka daukaka.
Bukatun dai na kunshe ne a cikin wasu kararraki masu lamba CV/395/M1/2025 da kuma CV/395/M2/2025, wadanda aka shigar a ranakun uku da kuma 25 ga watan Mayun 2025, wanda a cikinsu aka ambaci sunan Akpabio a matsayin mai daukaka kara.
DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a ManguWadanda ake kara kuma su ne Sanata Natasha da Magatakardar Majalisar Dokoki ta Kasa da Majalisar Dattawa da shugaban kwmaitin da’a, ladabtarwa da korafe-korafen jama’a na majalisar, Sanata Neda Imasuem.
Tun farko dai a cikin karar, Akpabio ya nemi kotun da ta kara masa lokacin da zai iya kalubalantar hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke mai lamba FHC/ABJ/CS/384/2025, wanda ta yanke ranar 10 ga watan Maris 2025 bisa hujjar cewa akwai kura-kurai a cikinsa.
Sai dai da take yanke nata hukuncin, kotun ta ce ta amince da bukatar janye kararrakin guda biyu, kamar yadda mai kara ya bukata.
Sai dai ta ce ta ci mai karar tara Naira 100,000, wadanda za a ba wacce aka yi kara.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
Aƙalla jihohi 11 na Najeriya sun kashe sama da Naira biliyan 6.2 wajen tallafa wa Alhazansu domin sauƙaƙa musu wajen zama a ƙasar Saudiyya yayin gudanar da aikin Hajjin 2025.
Wannan tallafi ya haɗa da kuɗi, jakunkunan tafiya, da kuma sayen raguna na hadaya domin sallar Layya.
Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APCGwamnatin Jihar Sakkwato ce ta fi kowa bayar da tallafi mafi yawa, inda Gwamna Ahmed Aliyu, ya bai wa kowane daga cikin alhazai 3,200 na jihar Riyal 1,000 (kimanin Naira 450,000).
A Kano kuwa, kowane alhaji daga cikin alhazai 3,345 sun samu kyautar Riyal 50.
Gwamnatin Jihar Legas ta bai wa kowane daga cikin alhazai 1,315 Riyal 180 (kimanin N74,870), yayin da Jihohin Jigawa da Kebbi suka bayar da mafi ƙarancin adadi.
Wani jami’in Gwamna Sanwo-Olu ya bayyana cewa: “Kowane Alhaji ya samu Riyal 180 a matsayin kyauta don sauƙaƙa rayuwarsu a lokacin aikin hajji.”
Jihar Borno ba ta bayar da kuɗi ba, amma ta biya kuɗin ragunan layya (hadaya) na Alhazan jihar guda 2,174.
Haka kuma, hukumomin Kano sun sanar da cewa kowane Alhaji zai samu babbar jakar tafiya domin dawowarsa gida cikin sauƙi.
Sai dai masana da malamai sun soki irin wannan kashe-kashen kuɗi da gwamnati ke yi, inda suka bayyana hakan a matsayin almubazzaranci da rashin fifita abin da ya fi muhimmanci.
Farfesa Yahaya Tanko, masani a harkokin siyasa, ya ce: “Wannan ba fifiko ba ne. Ya kamata gwamnoni su mayar da hankali kan matsalolin tsaro da talauci, ba tare da kashe kuɗi kan aikin hajji ba.”
Ya ƙara da cewa: “Al’umma na fama da sace-sace, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu, amma gwamnoni na kashe miliyoyi kan aikin Hajji. Wannan ba daidai ba ne.”
Hakazalika, babban malamin addini, Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce: “Kuɗaɗen da aka kashe a kan Hajji za a iya amfani da su wajen taimaka wa ‘ya’yan Alhazai su yi karatu. Wannan zai amfanar da iyalai da kuma al’umma gaba ɗaya.”
Mutane da dama a kafafen sada zumunta sun bayyana irin wannan kashe kuɗi a matsayin rashin adalci ga talakawa.
Wasu sun ce aikin Hajji ibada ce da ya kamata mutum ko al’umma su ɗauki nauyinta da kansu, ba gwamnati ba.
Yanzu haka ana ta kira ga gwamnoni da su dawo da hankali kan tsaro, kiwon lafiya, da ilimi domin hakan ne zai amfani mafi yawan jama’a, ba wasu ƙalilan da suka samu damar zuwa aikin Hajji kawai ba.