Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta ce za ta dauki nauyin dalibai ‘yan asalin yankin su 80 da ke kwalejin Ilmi ta tarayya ta Jama’are a Jihar Bauchi, da kwalejin fasaha ta Dutse da kuma kwalejin fasahar sadarwa ta Kazaure.

Shugaban Karamar Hukumar, Dr. Muhammed Uba Builder ya bayyana haka ga manema labarai a Birnin Kudu.

Dr Muhammad Uba, yayi bayanin cewar, an zabo mutum uku-uku daga kowace mazaba goma sha daya dake yankin.

Yana mai cewar, Karamar Hukumar ta yanke shawarar hakan ne domin bai wa dalibai damar karatu cikin sukuni.

Dr Muhammad Uba Builder, ya kara da cewar nan gaba kadan Karamar Hukumar za ta kara zabo wasu daliban dan tafiya manyan jami’o’i dake kasar nan.

A cewarsa, an kafa kwamati dan tantancewa daliban da suka cancanta.

A nasa jawabin Shugaban kwamatin tantance daliban kuma shugaban ma’aikata na yankin Yarima Musa, ya ce za su zabo daliban da suka cancata domin tura su makarantun da suka dace.

Ya kuma ya yabawa Shugaban Karamar Hukumar ta Birnin Kudu bisa namijin kokarinsa wajen daukar nauyin karatun daliban domin samun ingantacciyar rayuwa mai amfani a nan gaba.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Dole Ne A  Dauki Kwararan Matakan Don Dakatar Da Laifukan Gaza

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Dole ne a dauki kwararan matakai don dakatar da laifukan da ake yi a Gaza

A yayin ganawarsa da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif da tawagarsa a yammacin yau, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada wajabcin gudanar da ayyukan hadin gwiwa da inganci tsakanin kasashen Iran da Pakistan domin dakile laifukan da yahudawan sahayoniyya suke aikatawa a Gaza.

A farkon taron, Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana matsayin Pakistan na musamman a duniyar Musulunci, inda ya bayyana jin dadinsa da kawo karshen yakin da ake yi tsakanin Pakistan da Indiya, tare da bayyana fatansa na warware sabanin da ke tsakanin kasashen biyu ta hanyar lumana.

Haka nan kuma ya yi ishara da matsayar da Pakistan ta dauka kan batun Falastinu a cikin wadannan shekaru da suka gabata, yana mai cewa: Duk da cewa a cikin ‘yan shekarun nan a kodayaushe ana fuskantar kalubale ga kasashen musulmi na kulla alaka da yahudawan sahayoniyya, Pakistan ba ta taba samun irin wadannan fitintinu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Birtaniya ta dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami’an Zimbabwe
  • Amurka za ta hana ‘’visa’’ ga daliban dake sukanta a shafukan sada zumunta
  • Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan
  •  Nigeria: Mutane Da Yawa Sun  Rasa Rayukansu Sanadiyyar Harin Makiyaya A Jihar Benue
  • Tinubu na neman ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Dole Ne A  Dauki Kwararan Matakan Don Dakatar Da Laifukan Gaza
  • Sojojin Sudan Sun Fatattaki Dakarun Kai Daukin Gaggawa Daga Sansaninsu Da Ke Birnin Omdurman
  • NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji