Birgadiya Janar Rasul Sanaei-Rad wanda shi ne babban kwamandan sojan kasa na Iran ya bayyana hakan ne a wurin tunawa da zagayowar ranar ‘yanto da garin Khurramshahr daga mamaya sojojin Ba’asiyya na Sadam, a lokacin kallafaffen yaki.

Birgediya janar Sanaei -Rad ya kuma yi ishara da ‘yanto da garin na Khurramshar yana mai kara da cewa; yadda al’ummar Iran su ka yi gwagwarmayar ‘yanto da garin Khurramshahr, bayan tsawon shekaru 8 na yaki, ya sa Amurka ta fahimci cewa yaki da Iran yana da tsada da kuma hatsari; kuma da ace sun san za su yi nasara ta hanyar karfin soja da ba su zauna akan teburin tattaunawa ba.

Janar Sanaei ya kuma yi kira ga al’ummar Iran da su yi tsayin daka wajen fuskantar Amurka da wuce gona da irinta, kamar yadda su ka yi a lokacin yakin tsaron kasa mai tsarki wanda ta dauki shekaru takwas ana yi, da kasashen turai su ka goyi bayansa.

Haka nan kuma ya yi kira da a kare cigaban da aka samu a fagen fasahar makamashin Nukiliya.

Birgediya janar Sanaei-Rad ya kuma ce; Kare karamarmu a wannan lokacin da kuma manufofinmu na nan gaba, suna tana tattare da yin gwagwarmaya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos

Mazauna garin Jos sun shiga cikin zullumi bayan da jami’an Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) suka yi ta harbe-harbe a ranar Asabar.

Jami’an na Sibil Difens da ke aiki karkashi Hukumar Kula da Ci-gaban Garin Jos (JMDB) sun bude wuta ne a yayin wani samame da suka kai katafare shagon sayar da kayayyaki na S.O Plaza, lamarin da ya haifar da rikici.

Jami’an hukumar sun kuma lakada wa wani matashi mai aiki a plazar duka, lamarin da ya rincabe zuwa tayar da jijiyoyin wuya.

A yayin samamen, jami’an tsaron sun ce sun je ne domin kama wata babbar mota da ta keta dokar  hana manyan motoci shiga garin.

Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno

Amma wani bidiyo da ke yawo ya nuna cewa an ajiye motar ce a cikin harabar plazar kuma ba ta tare hanya ba.

Mazauna garin Jos sun bayyana cewa ba jami’an da ke aiki da JMDB sun yi kaurin suna wajen yin irin haka, inda suke lalata dukiyar jama’a a yayin samamen da suk kaiwa tare da nuna karfin makamai, da ke jefa jama’a cikin firgici.

Mamallakin S.O Plaza, Mista Solomon Okeke, the owner of S.O Plaza, ya bayyana abin a matsayin barna.

Ya kara da cewa ko a watan Agustan bara, wani Manajan Hukumar JMDB, Hart Bankat, ya jagoranci jami’an Sibil Difens zuwa plazar ya sa suka harbe tayoyi shida na wata babbar mota a cikin harabar wurin, wanda ya jawo musu asarar miliyoyin kudade.

Mista Okeke ya bayyana cewa jami’an “sun yi awon gaba da wata babbar mota cike da kaya, kuma sun yi wa wani dan shekara 19 duka suka yayyaga masa kaya, kuma har yanzu ba a san inda yak ba.

“Me ya sa duk lokacin da suka zo sai sun yi ta harbe-harbe suna dukan ma’aikata sun lalata dukiyar jama’a?”

A nasu bangaren, mazauna yakin na Bukuru sun bukaci Gwamna Caleb Mutfwang ya sanya baki tare da taka wa jami’an JMDB burki kan irin yadda suke wuce gona da iri domin a samu zaman lafiya.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin Janar Manajan JMDB, Akitet Hart Bankat, amma har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoton haka bai samu ba, saboda jami’in bai ba da amsa ga tambayar da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gargadi Shugaban Amurka Dangane Da Fadawa Iran Da Yaki
  • Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos
  • Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci
  • Iran Ta Ce: Amurka Ba Ta Fadan Hakikanin Abubuwan Da Aka Tattauna A Zamanta Iran 
  • ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum
  • Amurka Tana Takurawa JMI Don Biyan Bukatun HKI Na Ta Dakatar Da Shirinta Na Nukliya
  • Iran: Inda Makiya Kasar Sun San Cewa Zasu Sami Nasara A Kan Iran A Yaki Da Tuni Sunn Farmata Da Yaki
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
  • Limamin Masallacin Jumma’a A Nan Tehran Ya Yi Magana Dangane Da Kwatar Garin Khurramshar Daga Sojojin Sadam