Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi
Published: 24th, May 2025 GMT
Alkaluman da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ta samar a kwanakin baya sun shaida cewa, tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da tsarin samar da rangwamen gwamnati ta musayar sabbin motoci da tsofaffi, yawan bukatun da aka mika na yin musayar tuni ya wuce miliyan 10, matakin da ya yi matukar rage kudin da masu sayayya suka biya, baya ga kuma karuwar motocin da kamfanonin sai da motoci na gida da waje suka sayar.
Lamarin hakan yake ma ga kasuwar sai da Kayayyakin laturoni na amfanin yau da kullum a gidaje. In mun dauki misali da dandalin sai da kayayyaki na Suning.com, tun bayan da aka fara aiwatar da tsarin samar da rangwamen gwamnati ta musayar sabbin kayayyaki da tsofaffi a watan Satumban bara, yawan kayayyakin laturoni na amfanin yau da kullum a gidaje masu tamburan gamayyar jarin Sin da waje da aka sayar ya karu da kaso 44.7%. Wato ke nan kamfanoni masu jarin waje ma sun amfana da tsarin nan da aka aiwatar.
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar? Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A FaransaMa iya cewa tallafin da aka samar ta fannin manufofi da ma kwaskwarima da aka yi wa kasuwannin kasar Sin, ya samar da babbar dama ga kamfanoni masu jarin waje.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sabon Fira Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
Sabon fira ministan kasar Sudan Kamil Idris ya yi kira ga kasashen waje masu taimaka wa dakarun daukin gaggawa “RSF” da su kawo karshen taimakon da suke bawa masu aikata laifi.”
Idris wanda yake jawabin bayan kama aiki a jiya ya ce; Jami’an tsaro da kuma mahukuntan kasar ta Sudan suna da cikakken goyon baya a kasar don kawo karsehn ‘yan tawaye, masu dauke da makamai.”
Idris ya kuma ce; A shirye yake ya yi wa kasa aiki a cikin kekyawar anniyya da kwazo.”
Gwamantin kasar Sudan dai tana zargin Hadaddiyar Daular Larabawa da taimaka wa dakarun kai daukin gaggawa “RFS” wacce ta dauki shekaru biyu tana fafatawa da sojojin kasar.
Wasu daga cikin kasashen da Sudan take zargi da hannu a tawayen na “RSF” sun hada da Chadi, Libya da Sudan Ta Kudu.
Wasu rahotannin suna nuni da cewa, suna bawa wannan kungiyar makamai ne ta kan iyakokin da su ka hada wadannan kasashe da Sudan.
Tun barkewar yakin basasa a kasar Sudan a ranar 15 ga watan April 2023, zuwa yanzu adadin mutanen da su ka rasa rayukansu sun kai 24,000, yayin da wasu fiye da miliyan 14 su ka zama ‘yan gudun gijira, miliyan 4 daga cikinsu sun fice daga kasar, zuwa kasashen makwabta.