Guterres: MDD Ba Za Ta Shiga Duk Wani Shiri Da Ba Zai Girmama Dokokin Kasa Da Kasa Ba A Gaza
Published: 24th, May 2025 GMT
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa; MDD ba za ta shiga cikin duk wani tsari da ba zai girmama dokokin kasa da kasa ba a Gaza.
Bayanin nasa dai ya zo ne a matsayin mayar da martani akan maganar da ta fito daga HKI na cewa tana aiki tare da Amurka domin raba kayan agaji a Gaza.
Babban magatakardar MDD ya kuma kara da cewa; kaso 80% na yankin Gaza, ko dai yana karashin mamayar Isra’ila da kuma wanda aka bai wa mazaunansa umarnin su fice daga cikinsa.
Antonio Guterres ya yi gargadin cewa matukar ba a bude iyakoki ba, aka kuma shigar da kayan agaji, to mutanen Gaza za su rasa rayukansu.”
Babban magatakardar MDD ya tunawa HKI cewa, a matsayinta na ‘yar mamaya, wajibi ne ta mutunta fararen hula da kare karamarsu kamar yadda dokokin kasa da kasa su ka tanada.”
Haka nan kuma ya yi kira da a dakatar da yaki a cikin gaggawa,kuma wajibi ne a yunkura a yanzu domin a kowace rana ana kara samun wadanda suke rasa rayukansu da kuma jikkata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp