‘Yan Fansho Na FRCN Da NTA Sun Yabawa Gwamnati Bisa Amincewa Da Biyan Harkokinsu
Published: 21st, February 2025 GMT
Ma’aikatan Gidan Rediyon Tarayya (FRCN) da na Hukumar Gidan Talabijin ta Najeriya (NTA) da suka yi ritaya, sun bayyana jin dadinsu kan karin haske da Ministar Kudi ta yi game da wadanda za su ci gajiyar Naira Biliyan 758 da aka amince da su don biyansu kudaden fansho da suke bi.
A tsokacin da suka yi game da lamarin a Kaduna, ’yan fanshon sun bayyana cewa, bayanin ya tabbatar da cewa za a raba kudaden ne zuwa sassa biyu na ma’aikatan da suka yi ritaya a karkashin hukumar fansho ta PTAD da kuma shirin bayar da gudunmawar fansho (CPS).
Sun bayyana fatan cewa za a biya kudaden kafin karshen watan da ake ciki, domin baiwa ‘yan fansho damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin kwanciyar hankali da walwala.
Tsohon babban jami’in tsaro na NTA, Alhaji Abdullahi Umar, ya yabawa gwamnatin tarayya bisa wannan tabbacin da ta bayar, ya kuma bukaci kungiyoyin ‘yan fansho da su sanya ido sosai kan yadda ake biyan kudaden domin kaucewa duk wata matsala.
Ya kuma yi kira da a saka ‘yan fansho a cikin shirin inshorar lafiya na kasa (NHIS), wanda a baya aka dawo da shi, domin a taimaka musu wajen kula da lafiyarsu.
Suleiman Kaura
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp