An kaddamar da bikin baje koli na aikin noma da albarkatun dabbobi na kasa da kasa karo na 7 na kasar Cote d’Ivoire a cibiyar bukukuwan baje koli ta kasa da kasa dake birnin Abidjan, a jiya Jumma’a 23 ga wannan watan.

A matsayin muhimmiyar bakuwar kasa a gun bikin baje kolin, kasar Sin ta kafa rumfarta a tsakiyar cibiyar, inda aka gwada fasahohin zamani na aikin noma da injuna na kasar Sin.

Firaministan kasar Cote d’Ivoire Robert Beugre Manbe, ya bayyana a yayin bude bikin cewa, kasar Sin tana kan gaba a duniya a fannin fasahohin zamani na aikin noma. Kuma kasar Cote d’Ivoire za ta ci gaba da yin kirkire-kirkire kan fasahohin zamani don sa kaimi ga zamanantar da aikin noma a kasar da kuma inganta karfinta a wannan fanni.

Mataimakin ministan harkokin aikin noma da raya kauyuka na kasar Sin Zhang Xingwang, ya bayyana cewa, kasar Cote d’Ivoire ta fi samar da cocoa da dan yazawa (cashew nuts) da roba da sauran amfanin gona, kuma kasar Sin tana da babbar kasuwa, don haka bangarorin biyu suna da kyakkawar makoma kan hadin gwiwar fasahohin aikin noma, da samar da amfanin gona, da tattalin arziki da cinikayya da sauransu. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Cote d Ivoire

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

 

Ya kuma bayyana cewa kasar Sin wuri ne mai kyau ga harkokin zuba jari ga ‘yan kasuwa na duniya. Ya ce hadin gwiwa da kasar Sin yana nufin hadin gwiwa da damammaki, imani da kasar Sin yana nufin imani da kyakkyawar makoma, zuba jari a kasar Sin yana nufin zuba jari mai riba ta dogon zango.(Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan