Jaridar “Maariv” ta buga labarin da yake cewa; Tattauanwa a tsakanin “Isra’ila” da kasashen Afirka akan yadda za su bayar da dama ga mutanen Gaza da su yi hijira zuwa can, ta yi isa sosai.

 Rahoton jaridar na jiya Juma’a ya ci gaba da cewa; Tattaunawar ana yinta akarkashin damar da za a bai wa Mutanen Gaza  su yi hijira cikin zabin kansu, zuwa wasu kasashen na Afirka, kuma Amurka tana cikin wadanda ake tattaunawar da ita da wadannan kasashen na Afirka.

Haka nan kuma jaridar ta ‘yan sahayoniya ta ce, kasashen da ake tattaunawa da su, sun nuna amincewarsu a matakin na farko ka karbar bakuncin mutanen Gaza.

Tattaunawar dai ta kunshi yadda za a gina matsugunan Falasdinawan da za su yarda su yi hijirar, da kuma makarantunsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma

Ministan Harkokin wajen kasar Omman ya bada sanarwan cew za’a gudanar da tattaunawa zagaye na 5 tsakanin Iran da Amurka kan shirin Iran na makamshin nukliya a ranar 23 gawatan Mayun da muke ciki a birnin Roma nakasar Italiay.

Tashar talabijin ta Presstv a nnan Tehran ta ce Har yanzun ba’a ji tabakin kasashen biyu ba bayan wannan sanarwan.

Sai dai kafin haka Iran tace tana tunanin dakatar da halattan taron saboda yadda jami’an gwamnatin kasar Amurka suka bayyana cewa duk wata yarjeniya da Iran sai ta hada da hana ta tace Uranium.

Amma iran ta dage kan cewa ba zata bar hakkinta wanda yarjeniyar NPT ta bata ba na tashe Uranium karkashin kula na hukumar IAEA ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Yemen An Yi Gangamin Miliyoyin Mutane Na Nuna Goyon Bayan Falasdinawa
  •  MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi
  •  Nahiyar Afirka Ta Kafa Cibiyar Tattara Bayanai Akan Yanayi
  •   Ma’ariv: “Isra’ila” Ta Zama Saniyar Ware A Duniya
  • Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis
  • Yakin Gaza : Tarayyar Turai za ta sake nazari kan Yarjejeniyarta da Isra’ila
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan
  • An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka