Donal Trump Ya Kori Gomomi Daga Cikin Ma’aikata A Majalisar Tsaro Ta Kasar Amurka
Published: 24th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya sallami ma’aikata da dama a majalisar tsaron kasar Amuka saboda gazawarsu wajen magance wasu al-amuran tsaro da siyasa a kasar.
Tashar talabijin Ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Rauters yana cewa ma’aikatan maimakon su magance al-amuran tsaro da suka shafi tsaron kasa, sai sun zauna suna jiran abinda shugaban zai fada don su yi aiki a kansa.
Labarin ya kara da cewa shugaban ya dauki wannan matakin ne don ya mika wasu ayyukansu ga Pentagon da FBI da wasu ma’aikatun tsaro don magance wasu matsaloli masu muhimmanci a cikin sauri.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo
Zanga-zangar ta haifar da cunkoso a kan hanyar yayin da matafiya da suka hada da manyan motoci a kan titin suka tsaya cak na tsawon sa’o’i.
Matasan sun kuma koka da yadda har yanzu ba a sako wani jigo a jam’iyyar LP ba, Okasime Olowojoba da aka yi garkuwa da shi kusan wata guda duk da biyan sama da Naira miliyan 5 kudin fansa.
Daya daga cikin masu zanga-zangar Paul Lawani ya ce, “Ba za mu iya ci gaba da zama bayi a kasarmu ba, ya kamata gwamnati ta fada mana abin da take yi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp