Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya sallami ma’aikata da dama a majalisar tsaron kasar Amuka saboda gazawarsu wajen magance wasu al-amuran tsaro da siyasa a kasar.

Tashar talabijin Ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Rauters yana cewa ma’aikatan maimakon su magance al-amuran tsaro da suka shafi tsaron kasa, sai sun zauna suna jiran abinda shugaban zai fada don su yi aiki a kansa.

Labarin ya kara da cewa shugaban ya dauki wannan matakin ne don ya mika wasu ayyukansu ga Pentagon da FBI da wasu ma’aikatun tsaro don magance wasu matsaloli masu muhimmanci a cikin sauri.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka

Elon Musk, wanda ya taɓa zama mashawarcin Shugaban Amurka Donald Trump, ya ce zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa mai suna America Party.

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X (Twitter), makonni bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakaninsa da Shugaban Amurka.

Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya  Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano

Musk, wanda attajirin mai kuɗi sosai, ya ce jam’iyyarsa za ta kasance wata hanya ta daban daga jam’iyyu biyu da ake da su yanzu, wato Republican da Democrat.

Amma har yanzu ba a bayyana ko hukumar zaɓen Amurka ta amince da rajistar jam’iyyar ba.

Amma Musk bai bayyana wanda zai jagoranci jam’iyyar ko irin manufofinta ba.

Tun da farko Musk ya fara maganar kafa sabuwar jam’iyya ne bayan samun saɓani da Donald Trump, wanda hakan ya kai sa ga sauka daga matsayinsa a gwamnatin Trump.

Yayin wata ƙuri’ar jin ra’ayi da ya gudanar a X, mutane miliyan ɗaya ne suka kaɗa ƙuri’a, kuma kashi 60 daga cikinsu sun amince a kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Amurka Ta Soke Dokar Da Ta Tabbatar Da Hai’at Tarirusham Cikin Jerin Kungiyoyin Yan Ta’adda
  • Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka
  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda