2027: ’Yan Najeriya sun yi watsi da takarar Tinubu, sun koka kan tsadar rayuwa
Published: 23rd, May 2025 GMT
’Yan Najeriya daga kowane ɓangare daban-daban sun caccaki jam’iyyar APC bisa yanke shawarar goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2027, duk da cewa shekararsa biyu kacal da hawa mulki.
Wasu na ganin matakin ya nuna rashin tausayi da rashin damuwa da halin ƙuncin da al’umma ke ciki.
Jagororin jam’iyyar APC, gwamnoninta da ’yan majalisa ne suka fito suka nuna goyon bayansu ga Tinubu.
Amma jama’a na ganin hakan na nuna burin ci gaba da riƙe madafun iko ne kawai, ba wai taimakon talakawa ba.
Ra’ayoyi daga sassa daban-daban na NajeriyaA Jihar Legas, Mary Okonkwo, wata ’yar kasuwa ta ce: “Rayuwa na neman gagarar jama’a. Kasuwancina na shirin durƙushewa saboda hauhawar farashi. Kuma suna maganar zaɓe tun yanzu?”
Daga Fatakwal, Daniel Etim, ma’aikacin gwamnati ya ce: “Wannan goyon bayan da suka yi ya yi wuri da yawa, kuma ya nuna rashin mutunta mutane. Albashi ko mako ɗaya ba ya ishar mu.”
A Enugu, ɗalibar jami’a Adaeze Nnaji tambaya ta yi: “Shin wannan ne ladan wahalar da muke sha? Babu wutar lantarki, babu aiki, amma ana yaba wa shugaba wanda bai yi komai ba?”
A Abuja, Rashida Muhammad ta ce: “Tinubu ya ci amanarmu. Komai ya yi tsada kuma muna cikin tsananin wahala. Bai cancanci wa’adi na biyu ba.”
Tafawa Muhammad, wani manomi a Kano ya ce: “Farashin abincin kifi da taki ya ninka sau uku. Aikin gona na ya kusa durƙushewa.”
A Ibadan, Dele Olatunji, malamin makaranta ya ce: “Wadannan goyon baya ba don al’umma ba ne. Sun fi damuwa da kansu.”
Masana siyasa na ganin wannan goyon baya bai dogara da aiki ba, sai dai neman ci gaba da mulki.
Farfesa Hassan Saliu, ya gargaɗi cewa Najeriya na dab da zama ƙasa mai jam’iyya ɗaya.
Ya shawarci al’umma da su zauna cikin shiri domin su ɗauki mataki a 2027.
Wani masanin, Dokta Kabiru Sufi, ya ce ’yan siyasa sun fi mayar da hankali kan zaɓe fiye da warware matsalolin da ke addabar ƙasa, kamar tsaro, talauci da yunwa.
Duk da wannan goyon baya da jam’iyyar APC ta nuna, yawancin ‘yan Najeriya na buƙatar shugabanci na gari ne, ba wai alƙawura marasa amfani ba.
A cewar Adaeze Nnaji: “A gyara ƙasa tukunna sai a zo a yi maganar zaɓen 2027.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya Goyon Baya Siyasa Takara Watsi Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher
Kwamandan Runduna Kai Daukin Gaggawa ta kasar Sudan ya yi ikirarin kafa kwamitoci don binciken kisan kiyashin da aka yi a birnin El Fasher
Kwamandan Rundunar Kai Daukin Gaggawa ta Sudan (RSF), Muhammed Hamdan Dagalo “Hemedti,” ya amince a ranar Laraba cewa: Mayakansa sun aikata “keta haddi” a El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a yammacin Sudan. Ya yi ikirarin cewa: An kafa kwamitocin bincike kuma sun riga sun isa birnin domin fara ayyukansu.
A cikin wani jawabi na bidiyo, Hemedti ya ce, “Ya ga keta haddi da aka yi a El Fasher, kuma daga nan ya sanar da kafa kwamitocin bincike, ba kawai kafa kwamitoci ba, har ma kwamitocin bincike sun riga sun isa birnin na El Fasher domin fara ayyukansu.”
Hemedti ya yi ikirarin cewa: “Kwamitocin bincike na shari’a za su fara bincike nan take da kuma daukar alhakin duk wani soja ko jami’i da ya aikata keta haddi ko laifi ga duk wani mutum da aka kama, kuma za a sanar da sakamakon binciken nan take.”
Ya kuma yi ikirarin cewa: “Yanzu an ba da izinin gudanar da zanga-zangar farar hula a El Fasher gaba daya, kuma ana sake duba batun tsare fararen hula don tabbatar da sakin su duk inda aka tsare su. Waɗannan umarni ne da za a aiwatar nan take.”
Hemedti ya bukaci mazauna El Fasher “da su koma gidajensu da matsugunansu duk da cikas da ake samu a yanzu na tashin nakiyoyi da sauran ragowar matsalolin yaki.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin Faransa October 30, 2025 Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Amurka Ta Hana Marubuci Dan Nigeria Wole Soyinka Izinin Shiga Amurka October 30, 2025 Pakistan Tayi Barazanar Daukar Mataki Bayan Rushewar Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta Da Afghanistan. October 29, 2025 IRS: Sanya Sabbin Takunkumi Kan Kasar Iran Zai Haifar Da Mummunan Sakamakon A Yankin October 29, 2025 An saka dokar Ta Baci Bayan Barkewar Zanga-zanga A Zaben Shugaban Kasar Tanzaniya October 29, 2025 Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Tantance Sabbin Manyan Hafsoshin Sojin Kasar October 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci