An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja
Published: 25th, May 2025 GMT
Jami’an ’yan sanda tare da haɗin gwiwar ’yan sa-kai sun kama hakimin ƙauyen Guiwa da ke Ƙaramar Hukumar Mashegu a Jihar Neja.
Hakimin mai suna Garba Mohammed ana zarginsa da taimaka wa ’yan bindiga wajen aikata ta’addanci a yankin.
Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a IloriAn kama shi tare da wasu mutum 13 a safiyar ranar Juma’a da misalin ƙarfe 9 na safe, bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewar suna hannu wajen taikoman ’yan bindiga.
Rahotanni sun bayyana cewa hakimin yana bai wa ’yan bindiga mafaka a gidansa, inda suke taruwa suna shirya kai hare-haren.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar wa Aminiya kama hakimin ta wayar tarho.
Ya ce kama mutanen na daga cikin wani samame da ’yan sanda da ’yan sa-kai ke yi domin kawar da ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a yankin Mashegu.
A ranar 22 ga watan Mayu, 2025, rundunar ta kai samame dazukan Magaman-Daji da kewaye, inda suka fatattaki masu aikata laifi.
A ranar 23 ga watan Mayu, 2025 da misalin ƙarfe 9 na safe, rundunar ta sake afkawa ƙauyukan Guiwa da Telle bisa sahihan bayanai, inda aka kama hakimin Guiwa, Mallam Garba Mohammed, bisa zargin taimaka wa ’yan bindiga.
An gano babura huɗu da shanu 10 a gidansa, waɗanda ake zargin na ’yan bindiga ne.
Sauran mutum 13 an kama su a sassa daban-daban na Mashegu bisa zargin hannunsu a ta’addanci.
SP Abiodun, ya ce ana gudanar da bincike a kansu domin gano irin rawar da suka taka a ayyukan ta’addanci a yankin.
Ko da yake rundunar ba ta fitar da sunayen waɗanda aka kama ba, wani masani kan yaƙi da ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana sunayen wasu daga cikinsu.
Ya bayyana cewa akwai waɗanda suka fito daga ƙauyukan Wawa a Borgu, Gwajibo, Telle, Dukku a Rijau, Pallagi, Arera, Adogon Mallam da kuma Lumma.
Wani mazaunin New Bussa ya tabbatar wa Aminiya cewa an kama Alhaji Abdullahi Shehu daga Wawa da wasu mutum biyar daga Lumma.
Har yanzu ana ci gaba da bincike domin gano cikakken bayani kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga zargi yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta sanar da samun nasarar cafke Ifeanyi Eze Okorienta, wanda aka fi sani da “Gentle de Yahoo”, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar IPOB, a wani samame da ta kai a yankin kudu maso gabashin ƙasar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito wata majiya daga hedikwatar rundunar sojin tana cewa an cafke Gentle de Yahoo ne yayin farmakin da sojojin suka kai a ranar Lahadi kan sansanonin ’yan ƙungiyar a cikin wani dajin da ke ƙaramar hukumar Okigwe a Jihar Imo.
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a RibasMajiyar ta ce a yayin cafke jagoran na IPOB, an kuma ƙwato makamai da dama daga hannunsa, ciki har da bindigogi kirar Turai, harsasai, kakin sojoji da na ’yan sanda.
“Cafke wannan kwamanda babban ci gaba ne wajen murƙushe ayyukan ta’addanci da ƙungiyar IPOB ke aikatawa, musamman a yankunan da suke hana zaman lafiya,” in ji majiyar.
Kungiyar IPOB, wacce ke fafutukar ballewa daga Najeriya don kafa ƙasar Biyafara, ta kasance a gaba-gaba wajen aikata hare-hare da ta da tarzoma a jihohin kudu maso gabas, musamman ta hannun sashen rundunar da suka kafa da kansu mai suna Eastern Security Network (ESN).
Ana dai zargin cewa Eze yana ɗaya daga cikin jagororin da ke tsara harin kwantan bauna, da hana zirga-zirga a wasu sassan yankin, wanda hakan ya jefa al’umma cikin fargaba da zaman ɗar-ɗar.
Wannan nasara na zuwa ne bayan makonni kaɗan da wata kotu a ƙasar Finland ta yanke wa Simon Ekpa, wani babban jigo a ƙungiyar IPOB, hukuncin ɗaurin shekaru shida a gidan yari kan laifukan da suka shafi ta’addanci da tayar da zaune tsaye.
Masu sharhi na ganin cewa cafke Gentle de Yahoo wata alama ce da ke nuna cewa ana shirin ragargaza ƙungiyar IPOB gaba ɗaya, duk da cewar har yanzu akwai sauran rina a kaba, musamman ganin cewa wasu sassan yankin na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro.