Aminiya:
2025-07-08@07:50:15 GMT

An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya

Published: 23rd, May 2025 GMT

Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya, NRC ta tabbatar da kama ma’aikacinta mai suna Gift Eseeli, mai shekara 38, bisa zargin satar waya a Rafa Yard da ke kan hanyar Warri-Itakpe a harabar tashar jirgin ƙasa (WITS) Jihar Delta.

Jami’an rundunar Man O’war na shiyyar Railway Command ne suka kama ma’aikacin.

A cewar mai magana da yawun hukumar ta NRC, Callistus Unyimadu, binciken farko na nuni da cewa an cire dogayen wayoyin da suke ba da sigina masu sulke mai tsayin 50mm daga na’urorin gefen titin kafin jami’an ‘yan banga ƙarƙashin jagorancin Mista williams Agiake su cafke wanda ake zargin.

2027: ’Yan Najeriya sun yi watsi da takarar Tinubu, sun koka kan tsadar rayuwa Cutar lamoniya ta kama alhazai 99 ’yan ƙasar Indonesiya a Saudiyya

An gano kayayyakin da aka sace, kuma an miƙa su ga rundunar ’yan sandan Najeriya inda ta fara gudanar da cikakken bincike.

Manajan Darakta na NRC Dakta kayode Opeifa, a cikin sanarwar ya yi Allah wadai da faruwar lamarin tare da jaddada cewa waɗanda aka samu da laifin lalata dukiyar ƙasa za su fuskanci fushin doka.

“Kadarorin titin jirgin ƙasa mallakin kadarorin ƙasar Najeriya ne. Ayyukan ɓarna na barazana ga lafiyar fasinjoji tare da yin zagon ƙasa ga ayyukan muradun sabuwar Najeriya na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”

Ya ce, Hukumar ta NRC za ta gurfanar da duk wani mutum ko ƙungiya ciki har da ma’aikatan da aka samu da laifin yin ɓarna ba tare da ƙetare iyaka ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Tinubu Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya Jihar Kogi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC — Atiku Ko Peter Obi

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

‘Yan Najeriya suna ci gaba da tafka muhawara a kan  wanda jamiyyar hadaka ta ADC zata tsayar takarar Shugaban Kasa a zaben 2027.

 

Yayin da wasu suke ganin Atiku Abubakar yana da dimbin magoya baya, wasu kuwa gani suke yi shi ma Peter Obi ba kanwar lasa bane.

Ko me zai faru idan daya daga cikin su ya samu tikitin tsayawa takara a 2027?

NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a? DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wannan lamari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC — Atiku Ko Peter Obi
  • Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  • Majalisar Jihar Jigawa Ta Bukaci Karamar Hukumar Roni Ta Samar Da Karin Ajujuwa Ga Fulani Makiyaya
  • Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
  • An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano