An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya
Published: 23rd, May 2025 GMT
Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya, NRC ta tabbatar da kama ma’aikacinta mai suna Gift Eseeli, mai shekara 38, bisa zargin satar waya a Rafa Yard da ke kan hanyar Warri-Itakpe a harabar tashar jirgin ƙasa (WITS) Jihar Delta.
Jami’an rundunar Man O’war na shiyyar Railway Command ne suka kama ma’aikacin.
A cewar mai magana da yawun hukumar ta NRC, Callistus Unyimadu, binciken farko na nuni da cewa an cire dogayen wayoyin da suke ba da sigina masu sulke mai tsayin 50mm daga na’urorin gefen titin kafin jami’an ‘yan banga ƙarƙashin jagorancin Mista williams Agiake su cafke wanda ake zargin.
2027: ’Yan Najeriya sun yi watsi da takarar Tinubu, sun koka kan tsadar rayuwa Cutar lamoniya ta kama alhazai 99 ’yan ƙasar Indonesiya a SaudiyyaAn gano kayayyakin da aka sace, kuma an miƙa su ga rundunar ’yan sandan Najeriya inda ta fara gudanar da cikakken bincike.
Manajan Darakta na NRC Dakta kayode Opeifa, a cikin sanarwar ya yi Allah wadai da faruwar lamarin tare da jaddada cewa waɗanda aka samu da laifin lalata dukiyar ƙasa za su fuskanci fushin doka.
“Kadarorin titin jirgin ƙasa mallakin kadarorin ƙasar Najeriya ne. Ayyukan ɓarna na barazana ga lafiyar fasinjoji tare da yin zagon ƙasa ga ayyukan muradun sabuwar Najeriya na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”
Ya ce, Hukumar ta NRC za ta gurfanar da duk wani mutum ko ƙungiya ciki har da ma’aikatan da aka samu da laifin yin ɓarna ba tare da ƙetare iyaka ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Tinubu Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya Jihar Kogi
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A yau ne Gwamna Siminalaye Fubara ke dawowa kujerarsa a matsayin gwamnan Jihar Ribas bayan dakatarwa da ayyana dokar ta baci na watanni shidda da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi a jihar.
Manazarta dai na hasashen wannan dawowar zata bude wani sabon babi a siyasar jihar Ribas.
NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaYayin da wasu ke ganin gwamna Fubara zai koma bakin aiki ne ya cigaba da gudanar da mulkin jihar kamar yadda ya barta, wasu kuwa gani sukeyi akwai babban kalubale dake gaban gwamnan.
Domin sauke shirin, latsa nan