Kafafen watsa labarun HKI sun ce, Amurka ta bayyana cewa, MDD ta ki aiki tare da kamfanonin Amurka da na Isra’ila domin raba kayan agaji a Gaza.

Majiyar ta HKI ta kuma kara da cewa; An jinkirta aiwatar da Shirin na raba kayan agajin saboda wasu dalilai na kayan aiki.

Wuraren hudu ne dai aka ware domin raba kayan agajin a kudancin Gaza, an kuma kai shi zuwa mako na gaba.

Wasu kafofin watsa labaru sun ambato babban magatakardar MDD yana cewa; MDD ba za ta shiga cikin duk wani shiri a Gaza wanda ba zai girmama dokokin kasa da kasa ba.

 A cikin wani bayani da wata kungiya mai kula da iyalai a yankin Gaza ta fitar, ta nuna kin amincewarta da tsallake kungiyoyin kasa da kasa a wajen raba kayan agajin.

Ana zargin Amurka da HKI da kokarin tattara bayanai akan fuskoki, idanu da kuma DNA na iyalan da za a bai wa tallafin abinci, da hakan zai bayar da damar cutar da Falasdinawan Gaza da kuma kashe wanda suke so a nan gaba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

A jawabinsa yayin Kaddamar rabon kayan Sanata Muhammadu Adamu Aliero ya bayyana cewa “Komawar mu jam’iyyar APC ya nufin kawar da adawa don samar da ci gaba a jihar Kebbi, kuma zamu yi hadin gwiwa da gwamnatin, Gwamna Nasir Idris don amfanin mutanenmu ga irin ayyukan da ya gudanar a dukkan kananan hukumomin 21 na jihar, Wanda shi ne muke kira a ko da yaushe cewa a samar da cigaba ga jama’ar da muke shugabanta,” Inji Sanata Muhammadu Adamu Aliero.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta yi tir da kiran da dan majalisar dokokin Amurka ya yi na kai farmakin nukiliya a Gaza
  • Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu
  • Guterres: MDD Ba Za Ta Shiga Duk Wani Shiri Da Ba Zai Girmama Dokokin Kasa Da Kasa Ba A Gaza
  • Maariv: Tattaunawa A Tsakanin “Isra’ila” Da Kasashen Afirka Ta Yi Nisa Akan Hijirar Mutanen Gaza
  • Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji
  • Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
  • Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka