Kafafen Watsa Labarun Isra’ila: Kungiyoyin Kasa Da Kasu Sun Ki Shiga Cikin Shirin Isra’ila Da Amurka Na Raba Kayan Agaji
Published: 25th, May 2025 GMT
Kafafen watsa labarun HKI sun ce, Amurka ta bayyana cewa, MDD ta ki aiki tare da kamfanonin Amurka da na Isra’ila domin raba kayan agaji a Gaza.
Majiyar ta HKI ta kuma kara da cewa; An jinkirta aiwatar da Shirin na raba kayan agajin saboda wasu dalilai na kayan aiki.
Wuraren hudu ne dai aka ware domin raba kayan agajin a kudancin Gaza, an kuma kai shi zuwa mako na gaba.
Wasu kafofin watsa labaru sun ambato babban magatakardar MDD yana cewa; MDD ba za ta shiga cikin duk wani shiri a Gaza wanda ba zai girmama dokokin kasa da kasa ba.
A cikin wani bayani da wata kungiya mai kula da iyalai a yankin Gaza ta fitar, ta nuna kin amincewarta da tsallake kungiyoyin kasa da kasa a wajen raba kayan agajin.
Ana zargin Amurka da HKI da kokarin tattara bayanai akan fuskoki, idanu da kuma DNA na iyalan da za a bai wa tallafin abinci, da hakan zai bayar da damar cutar da Falasdinawan Gaza da kuma kashe wanda suke so a nan gaba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
A jawabinsa yayin Kaddamar rabon kayan Sanata Muhammadu Adamu Aliero ya bayyana cewa “Komawar mu jam’iyyar APC ya nufin kawar da adawa don samar da ci gaba a jihar Kebbi, kuma zamu yi hadin gwiwa da gwamnatin, Gwamna Nasir Idris don amfanin mutanenmu ga irin ayyukan da ya gudanar a dukkan kananan hukumomin 21 na jihar, Wanda shi ne muke kira a ko da yaushe cewa a samar da cigaba ga jama’ar da muke shugabanta,” Inji Sanata Muhammadu Adamu Aliero.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp