Shugaban Wanda Alhaji Ahmed Aliyu Zarma ya wakilta ya kara da cewa, wannan cibiya ba itace ta farko ba da shugaban ya fara ginawa ba, a cewarsa ya gina irinsu a sassa daban-daban a fadin kasar nan. Yana Mai Cewa, baya ga cibiyoyin koyar da addinin musulunci ya samar da makarantu a majami’un addnin kirista da gyaran makarantu da kuma tallafawa marayu da marasa galihu a cikin al’umma.

Zarma ya ce, sama da shekaru goma shugaban yana gudanar da irin wadannan Ayyukan tallafawa Rayuwar al’umma musamman marayu da marasa galihu a fadin kasar nan Baki daya.

Sarki Musulmi tare da Sarkin Zazzau a wurin taron

A nasa jawabin, Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubukar lll Ya jinjiwa shugaban na DSS na ginawa da sadaukar da makarantar ga alummar musulmi duk da cewa, shi shugaban ba musulmi ba ne. Yace, “babu wata kasa a fadin Duniya da kirista da musulmi suke zama bisa fahimtar juna kamar Nijeriya”, inda yace hakan yana nuni da cewa abubuwa za su gyaru a kasar nan.

 

Sarkin Musulmi yace babu shakka lokaci ya kusa da za’a samu saukin rayuwa a fadin kasar nan duk da cewa al’umma suna fama da kuncin rayuwa.

 

A zantawarsa da manema labarai Jim kadan bayan kammala taron, shugaban kwamitin shirya taron, Shek Yusuf Sambo Rigachikun, ya yaba da kokarin shugaban DSS na sadaukar da makarantar ga al’ummar musulmi inda yace, matsayinsu na malaman addini zasu tabbatar da cewa an Samar da ilimi Mai nagarta da kula da tarbiyyar daliban dake karatu a makarantar.

 

Mahalarta taron sum hada da Mai Alfarma Sarkin Musulumi, Sultan Muhammadu Sa’ad Abubakar III; Ministan kasafin kudi, Abubakar Atiku Bagudu; Mataimakiyar Gwamnan Jihar kaduna, Hadiza Sabuwa Balarabe; Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli; Sarkin Birnin Gwari, Malam Zubairu Jibrin Mai Gwari, da dai sauran manyan Baki daga sassa daban-daban na kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 

 

 

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya bukaci hukumomin tsaro da Sarakuna da kuma kungiyoyin matasa su dauki matakan gaggawa wajen dakile gina gine-gine a karkashin manyan layukan lantarki da kuma hana lalata kayan hasken lantarki.

 

Babban Manajan TCN na Yankin Kaduna, Injiniya Nasir Mansur Fada, ne ya yi wannan kira a yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar da masu ruwa da tsaki a hedikwatar TCN da ke Mando, Kaduna.

 

Taron ya samu halartar Sarakuna da jami’an tsaro da kungiyoyin masu zaman kansu domin bin umarnin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta kasa domin ci gaba da kokarin da TCN kiyi na dakile mamaye filayen layin lantarki da kare dukiyoyin kasa.

 

Injiniya Nasir Mansur Fada ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin al’umma da hukumomin da abin ya shafa domin samun wadataccen wutan lantarki a kasan nan.

 

Ya bayyana cewa an girka sababbin nauran bayarda wuta wato transformers a wurare daban-daban tare da ci gaba da ayyukan fadada samarda hasken wutan da kuma gyaran cibiyoyin wuta a fadin jihar Kaduna.

 

Sai dai ya kuka cewa hakka ba zata cimma ruwa ba mudin al’ummomin da ke zaune a kusa da cibiyoyin wutar suka gaza sanya ido domin kare kayyakin hasken lantarkin.

 

A cikin wata makala da aka gabatar mai taken Illar Lalata Kayan Wuta a Kasa, Manaja Mai Kula da Layyukan Wutan na Yankin Kaduna, Injiniya Simon Innocent, ya bayyana cewa ayyukan lalata kayan lantarki na haifar da matsaloli wajen samun wuta da kuma durkusar da ci gaban tattalin arzikin kasa.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Kwamandan Hukumar Tsaro ta Civil Defence (NSCDC), Ahmed Isah Audu, ya ce sanarda da jami’an akan lokaci da bayanai akan barnar da ake kan yi na da matukar muhimmanci wajen dakile ayyukan lalata kayan wuta a ko’ina cikin duniya.

 

An kammala taron wayar da kan ne tareda tattaunawa tsakanin mahalarta taron inda suka sha alwashin tallafa wa TCN tare da hada kai domin kare kayayyakin wuta da tabbatar da tsaro da ci gaba a al’umma.

COV: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda
  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
  • Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
  • Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi
  • Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara