Shugaban Wanda Alhaji Ahmed Aliyu Zarma ya wakilta ya kara da cewa, wannan cibiya ba itace ta farko ba da shugaban ya fara ginawa ba, a cewarsa ya gina irinsu a sassa daban-daban a fadin kasar nan. Yana Mai Cewa, baya ga cibiyoyin koyar da addinin musulunci ya samar da makarantu a majami’un addnin kirista da gyaran makarantu da kuma tallafawa marayu da marasa galihu a cikin al’umma.

Zarma ya ce, sama da shekaru goma shugaban yana gudanar da irin wadannan Ayyukan tallafawa Rayuwar al’umma musamman marayu da marasa galihu a fadin kasar nan Baki daya.

Sarki Musulmi tare da Sarkin Zazzau a wurin taron

A nasa jawabin, Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubukar lll Ya jinjiwa shugaban na DSS na ginawa da sadaukar da makarantar ga alummar musulmi duk da cewa, shi shugaban ba musulmi ba ne. Yace, “babu wata kasa a fadin Duniya da kirista da musulmi suke zama bisa fahimtar juna kamar Nijeriya”, inda yace hakan yana nuni da cewa abubuwa za su gyaru a kasar nan.

 

Sarkin Musulmi yace babu shakka lokaci ya kusa da za’a samu saukin rayuwa a fadin kasar nan duk da cewa al’umma suna fama da kuncin rayuwa.

 

A zantawarsa da manema labarai Jim kadan bayan kammala taron, shugaban kwamitin shirya taron, Shek Yusuf Sambo Rigachikun, ya yaba da kokarin shugaban DSS na sadaukar da makarantar ga al’ummar musulmi inda yace, matsayinsu na malaman addini zasu tabbatar da cewa an Samar da ilimi Mai nagarta da kula da tarbiyyar daliban dake karatu a makarantar.

 

Mahalarta taron sum hada da Mai Alfarma Sarkin Musulumi, Sultan Muhammadu Sa’ad Abubakar III; Ministan kasafin kudi, Abubakar Atiku Bagudu; Mataimakiyar Gwamnan Jihar kaduna, Hadiza Sabuwa Balarabe; Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli; Sarkin Birnin Gwari, Malam Zubairu Jibrin Mai Gwari, da dai sauran manyan Baki daga sassa daban-daban na kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

Da safiyar yau 17 ga watan Satumba, aka bude dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan karo na 12 da zai dauki kwanaki 3, daga raneku 17 zuwa 19 ga wannan nan, bisa jigon “daukaka tsarin duniya da inganta neman ci gaba cikin lumana”, a nan birnin Beijing.

Tawagogi sama da 100 na gwamnatocin kasashe daban-daban da yankuna da wakilan kungiyoyin kasa da kasa ne ke halartar taron, inda yawan masu rajista ya wuce 1,800.

Da safiyar yau, taron ya shirya tarukan tattaunawa guda 6 bisa jigon “ma’anar cimma nasarar yakin duniya na kin tafarkin murdiyya” da “madaidaitan hanyoyi da manyan kasashe za su bi na yin mu’ammala”, da “hanyoyin warware rikice-rikicen shiyya-shiyya”, da “cika shekaru 80 da kafuwar MDD: samun ci gaba cikin sauye-sauye”, da “amfani da sarrafa sabbin fasahohi”, da kuma “kirkire-kirkire a bangaren kimiyya da fasaha da sauye-sauyen yanayin yaki”. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar