Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi
Published: 25th, May 2025 GMT
Ministan ‘yan sandan kasar Afirka ta kudu, ya ce, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi na cewa an yi wa fararen fatar kasar kisan kiyashi a yayin ziyarar da shugaban kasar Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa ya kai.
A yayin ganawar da ya yi da shugaban kasar Afirka ta kudu, shugaban kasar Amurka ya kunna wani faifen bidiyo da a ciki aka nuna gicciye a gefen hanya domin tunawa da fararen fata manoma da aka yi wa ksian gilla.
Ministan ‘yan sandan kasar ta Afirka ta kuku Senzo Mchunu ta cewa; Wadannan gicciyen ba su nuni da cewa suna akan kabarurruka ne, ko wani wuri na tunawa da matatu, an Sanya su ne a 2020 domin tunawa da dukkanin manoman da aka kashe a fadin kasar ta Afirka ta kudu.
Har ila yau, ministan ‘yan sandan na kasar Afirka ta kudun ya kuma kara da cewa; ‘yan fashi da makami sun kashe wasu ma’aurata manoma a cikin gonarsu, yana mai kara da cewa; Abinda Trump ya yi shi ne murguda wancan labarin da kirkirar abinda ya kira; “Kisan Kiyashi.”
Mchunu ya kara da cewa; kasar Afirka ta kudu tana girmama mutanen Amurka da shugaban kasarta, amma ko kadan ba ta girmama kirkirarren labarin; Kisan Kiyashi.”
Amurka ta dauki wannan matakin ne dai a kan Afirka Ta Kudu saboda ta kai karar HKI akan kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Afirka ta kudu shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai
Babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne shugaban kasar, Mr. Xi Jinping, a kwanakin baya ya yi muhimmin bayani game da aikin raya harkoki masu nasaba da wayewar kai a kasarsa, inda ya ce, ci gaban dukkanin fannonin samar da ababen more rayuwa da kuma wayewar kai, muhimmiyar alama ce ta zamantarwa mai salon kasar Sin.
Shugaba Xi ya jaddada cewa, ya kamata a karfafa hadin kan jama’a bisa tunanin tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin na sabon zamani, da mai da hankali kan wayar da kan al’umma, da sa kaimin raya al’adu da kuma da’a a tsakanin al’umma, sa’an nan kuma a karfafa ayyukan ba da jagoranci, da zurfafa yin gyare-gyare da kirkire-kirkire, da sa kowa ya shiga wannan harka, domin samar da karin kuzari wajen gina kasa mai karfi da farfado da al’ummar kasar.
A yau Juma’a ne aka bude taron karrama wadanda suka ba da muhimmiyar gudummawa wajen raya wayewar kan al’umma a kasar Sin, inda kuma aka sanar da wannan muhimmin bayanin da shugaba Xi ya yi. (Lubabatu Lei)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp