HausaTv:
2025-11-02@16:59:21 GMT

Afirka ta Kudu: Ba Za Mu Janye Kararmu Kan Isra’ila A Kotun ICJ Ba

Published: 14th, February 2025 GMT

Afirka ta Kudu ta yi alkawarin ci gaba da shari’ar kisan kiyashi da ta shigar a gaban kotun ICJ a kan Isr’ila,  duk da umurnin da Donald Trump ya bayar na katse taimakon da Amurka ke ba kasar Afirka ta Kudu saboda matakin da ta dauka kan babbar kawar Amurka.

“Babu wata dama” kan janye karar ta  ICJ, ba tare da la’akari da duk wata barazana ko mataki da Trump zai dauka ba, a cewar ministan harkokin wajen Afirka ta Kudu Ronald Lamola, wanda ya kara da cewa, “Tsayawa a kan ka’idojinmu wani lokaci yana da sakamako, amma mun tsaya tsayin daka kan wannan batu, ganin cewa yana da muhimmanci ga duniya, da kuma bin doka da ka’ida.

Dokar da Trump ya sanya wa hannu ta dakatar da ba da taimako ga Afirka ta Kudu, ya kuma yi alkawarin ci gaba da daukar wasu matakan domin takura kasar Afirka ta kudu kan matakin shigar da kara da ta dauka a kan Isra’ila game da batun yakin Gaza.

Afirka ta Kudu ta gabatar da karar kisan kiyashi kan “Isra’ila” a karshen shekara ta 2023 zuwa kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, inda ta bukaci kotun kasa da kasa da ta dauki matakai kan mahukuntan Isra’ila saboda karya yarjejeniyar kisan kare dangi ta Majalisar Dinkin Duniya.

Ireland a hukumance ta shiga cikin shari’ar Afirka ta Kudu a watan Disamba 2024, kuma jim kadan bayan haka, Cuba ta sanar da aniyar ta na shiga cikin lamarin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025 Daga Birnin Sin Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi