A Yemen An Yi Gangamin Miliyoyin Mutane Na Nuna Goyon Bayan Falasdinawa
Published: 24th, May 2025 GMT
A jiya Juma’a miliyoyin mutane Yemen sun cika dandalin ” Saba’in” dake birnin Sanaa, domin nuna cikakken goyon bayansu ga al’ummar Falasdinu.
An bai wa gangamin taken: ” Muna tare da Gaza” domin jaddada ci gaba da nuna goyon bayan al’ummar Falasdinu da suke fuskantan kisan kiyashi daga sojojin HKI, da kuma nuna kin amincewa da jefa mutanen yankin cikin yunwa.
Masu gangamin sun yi tir da yadda kasashen larabawa da na musulmi su ka nuna gajiyawa da kuma yin abin kunya saboda yadda su ka yi shiru akan abinda yake faruwa da mutanen Gaza.
Bugu da kari a yayin wannan gangamin an yi jinjina ga sojojin kasar da suke kai wa HKI hare-hare da kakaba takunkumi akan tasoshin jiragen sama da na ruwa na “Ben Gorio” da kuma ” Haifa”.
Daga cikin wadanda su ka gabatar da jawabi a wurin gangamin da akwai ‘yan Afirka mazauna Yemen, inda su ka yi jinjina ga gagaruwar da Yemen din ke takawa waje taimakawa al’ummar Falasdinu.
Haka nan kuma sun bayyana cewa, batun Falasdinu ya shafi dukkanin musulmi, da masu ‘yanci a duniya baki daya, kuma batu ne na ‘yan adamtaka a matakin farko.”
Bugu da kari sun yi kira ga shugabannin nahiyar Afirka da ma al’ummarta da su kasance a tare da mutanen Gaza da ake zalunta, su taimake su wajen fuskantar zaluncin da ake yi musu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mai kwashe sharar da ya shekara 40 yana tara kuɗin Hajji ya isa Saudiyya tare da matarsa
Wani dattijo mai aikin kwashe shara da ya shekara 40 yana tara kuɗin domin zuwa aikin Hajji ya samu cika burinsa a bana.
A karshe dattijoin dan qasar Indosauke ya samu damar zuwa sauke farali inda ya isa Kasa Mai Tsarki tare da matarsa.
Wanni dattijon wanda ya nuna tsananin juriya da jajircewa ya bayyana yadda kwashe shekara 40 yana tara 1,000 na kuɗin ƙasarsu a kullum, domin tara kuɗin da zai sauke farali shi da mai ɗakinsa.
A yayin da ake yake hira da Kamfanin Dillancin Labarai na kasar Saudiyya bayan isarsu ƙasar domin sauke farali, dattijoin ya bayyana cewa tun ashekarar 1986 ya fara tara wannan kuɗi bayan samun goyon bayan matarsa.
Ya bayyana cewa a duk loƙacin da ya dawo daga aikinsa na kwashe shara sai ya ware wannan kuɗin domin cika masu burinsu.
Har wa yau ce duk da halin matsi da rashi da suke tsintar kansu a wasu lokuta wannan bai sa sun sauya ra’ayinsu na tara kuɗin Hajjin ba.