Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin siyasa ya bayyana cewa: Matsayin Amurka a cikin ɗakin tattaunawa da Iran ya bambanta da abin da suke shelantawa a waje

Majid Takht-Ravanchi mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin siyasa ya bayyana cewa: Kalamai da matsayar da jami’an Amurka suka dauka a cikin dakin tattaunawa da Iran suna shan bamban a fili da abin da suke bayyanawa a bainar jama’a, yana mai cewa wannan sabani yana dakushe kwarin gwiwar bangaren Iran da kuma yin barazana ga makomar shawarwarin.

A wata hira da ya yi da mujallar Der Spiegel ta Jamus, Takht-Ravanchi ya bayyana kin amincewar da Iran ta yi da bukatar “samar da sifili na Uranium da take sarrafawa”, yana mai jaddada cewa inganta sinadarin Uranium don manufar zaman lafiya wani muhimmin bangare ne na shirin makamashin nukiliyar Iran kuma wani hakki ne da ba za a iya tattaunawa kansa ba.

Yana mai jaddada cewa: “Idan har Amurka ta nace da batun dakatar da duk wani abu da ake yi na inganta sinadarin Uranium, to lallai tattaunawar da ake yi ba za ta kai ga gaci ba,” Ya kara da cewa: Tace sinadarin Uranium wani babban nasara ce ta kasa, kuma Iran ba za ta yi watsi da shi ba, yana mai jaddada cewa har yanzu ba a sanya batun wa’adin (kamar shekaru 25) kan teburin tattaunawa ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa dukkan kasashe mambobia a kungiyar ECO ta raya tattalin arziki na kasashen yankin sun yi tir da HKI a taron kungiyar wanda aka gudanar a birnin Khankendi. Na kasar Azerbaijan. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka bayan tawowarsa daga taron a daren jumma’a a kuma shafinsa na X. Shugaban ya kuma kara da cewa Tehran a shirye take ta hada kai da wadannan kasashe makobta don taimakawwa juna a dukkan bangarorin rayuwa wadanda suka hada da kyautata tattalin arzikin yankin da al-adu da sauransu.

Shugaban ya bayyana cewa yana godiya ga dukkan kasashen kungiyar ECO da kuma sauran kasashen yankin da sauran kasashen duniya wadanda suka nuna goyon bayansu ga kasarsa bayan yakin kwanaki 12 da HKI da kuma Amurka.

Daga karshe yace  yana fatan kasar da sauran kasashen kungiyar ECO zasu kai ga gurunsu na bunkasar tattalin arziki ta shekara ta 2035.

A ranar jumma’a 13 ga watan Yuni ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare a kan Iran inda suka kashe manya-manyan jami’an sojojin kasar da masana fasahar Nukliya da kuma fararen hula wadanda basu san hawa ko sauka ba. Sannan Amurka ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar da suke fordo Natanz da kuma Esfahan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Olubadan Na Ibadan Ya Rasu Yana Da Shekara 90
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran