Aminiya:
2025-07-08@08:10:35 GMT

Cutar lamoniya ta kama alhazai 99 ’yan ƙasar Indonesiya a Saudiyya

Published: 23rd, May 2025 GMT

Mutum daya ya rasu bayan da maniyyata 99 daga kasar Indonesiya suka kamu da cutar lamoniya a yayin da suka tafi aikin Hajji a Saudiyya. 

Ma’aikatar Lafiya ta kasar Indonesiya ta bayyana damuwa game da yawaitar kamu da cutar ta lamoniya a tsakanin maniyyatan nata.

Sanarwar da ta fitar ta bayyana cewa maniyyatan suna samun kulawa a asibitoci a biranen Makka da Madina tana mai kira da ga maniyyatan da su “kiyaye sosai, saboda lamarin na iya kara munana idan ba a yi maganinsa da wuri yadda ya kamata ba.

Shugabar Sashen Kiwon Lafiya na na Tawagar Aikin Hajjin Kasar, Liliek Marhaendro Susilo, ta danganta bullar cutar da tsananin zafi da gajiya da kuma cunkoson jama’a sai kuma matsalolin lafiya da jama’a ke fama da su.

Jami’an tsaro sun kashe ’yan ta’adda 13,000 daga 2023 zuwa yanzu —Ribadu Allah Ya Isa: Shugaban PDP Damagun ya musanta zargin yi wa APC aiki Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa

Don haka ta bukaci maniyyata da su dauki matakan sanya takunkumin rufe fuska da wanke hannuwansu da shan ruwa sosai da kuma shan magunansu yadda ya kamata. Sauran su hada da nisantar shan sigari da kuma saurin kai rahoton duk wata matsalar lafiya da suka samu domin a dauki mataki.

A nata bangaren, Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya ta sanar cewa maniyyatanta 25,075 sun tafi Makkah daga Madina sanye da katinsu na Nusuk, wanda hukumomin Saudiyya suka wajabta wa maniyyata sanyawa a matsayin katin shaidarsu. (Xinhua/NAN)

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Indonesiya lamoniya maniyyata Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala

Gangamin Ashura ya zama lamarin mafi girma da cunkoson jama’a inda tattakiin Tuwairij yake gudana tare da faɗaɗa da ba a taɓa ganin irinsa ba

Tattakin Tuwairij na bana zuwa birnin Karbala na fuskantar hallara da cunkoson jama’a da ba a taba ganin irinsa ba, inda dimbin masu ziyara  daga sassan duniya ke tururuwa zuwa hubbaren Imam Husaini da kuma titunan da ke kewaye.

Mai ba da shawara ga babban sakataren cibiyar Hubbaren Imam Husain {a.s} Fadel Oz a cikin wata sanarwa da ya aikewa kafafen watsa labarai ya bayyana cewa: “A shirye-shiryen wannan juyayi, babban Sakatariyar Haramin Imam Husain (a.s) da haramin Abbas sun samar da dukkan sharuddan da suka dace don kula da masu ziyara da kuma tabbatar da jin dadinsu.

Ya kara da cewa, “Yankin da aka kebe domin gudanar da juyayin Ashura  ya samu gagarumin ci gabata hanyar fadada shi, domin a shekarun da suka gabata ana ci gaba da gudanar da ayyukan da suka yi na mallakar wuraren da ke kewaye da fadada titunan da ke zuwa gare su da nufin daukar saukaka wa masu halartar taron.

Oz ya ci gaba da cewa “Hukumar ayyuka, ‘yan sanda, sassan jami’ai, da kuma cibiyoyin gwamnati sun kuma taka rawar gani wajen hada kai don tabbatar da gudanar da juyayin Ashura cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Ya bayyana cewa, “wannan hadin gwiwa yana nuna irin kishin da hukumomin da abin ya shafa suke da shi wajen tabbatar da nasarar gudanar da juyayin Ashura a cikin yanayi na musamman na ruhi,” yana mai jaddada cewa “wadannan fadadawa da shirye-shirye suna tafiya tare da ci gaba da karuwar masu ziyara da kuma tabbatar da samun kwarewa da kwanciyar hankali a wannan babban taron addini.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
  • Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya
  • Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin
  • Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar
  • An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano