Aminiya:
2025-05-23@19:12:36 GMT

Cutar lamoniya ta kama alhazai 99 ’yan ƙasar Indonesiya a Saudiyya

Published: 23rd, May 2025 GMT

Mutum daya ya rasu bayan da maniyyata 99 daga kasar Indonesiya suka kamu da cutar lamoniya a yayin da suka tafi aikin Hajji a Saudiyya. 

Ma’aikatar Lafiya ta kasar Indonesiya ta bayyana damuwa game da yawaitar kamu da cutar ta lamoniya a tsakanin maniyyatan nata.

Sanarwar da ta fitar ta bayyana cewa maniyyatan suna samun kulawa a asibitoci a biranen Makka da Madina tana mai kira da ga maniyyatan da su “kiyaye sosai, saboda lamarin na iya kara munana idan ba a yi maganinsa da wuri yadda ya kamata ba.

Shugabar Sashen Kiwon Lafiya na na Tawagar Aikin Hajjin Kasar, Liliek Marhaendro Susilo, ta danganta bullar cutar da tsananin zafi da gajiya da kuma cunkoson jama’a sai kuma matsalolin lafiya da jama’a ke fama da su.

Jami’an tsaro sun kashe ’yan ta’adda 13,000 daga 2023 zuwa yanzu —Ribadu Allah Ya Isa: Shugaban PDP Damagun ya musanta zargin yi wa APC aiki Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa

Don haka ta bukaci maniyyata da su dauki matakan sanya takunkumin rufe fuska da wanke hannuwansu da shan ruwa sosai da kuma shan magunansu yadda ya kamata. Sauran su hada da nisantar shan sigari da kuma saurin kai rahoton duk wata matsalar lafiya da suka samu domin a dauki mataki.

A nata bangaren, Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya ta sanar cewa maniyyatanta 25,075 sun tafi Makkah daga Madina sanye da katinsu na Nusuk, wanda hukumomin Saudiyya suka wajabta wa maniyyata sanyawa a matsayin katin shaidarsu. (Xinhua/NAN)

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Indonesiya lamoniya maniyyata Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano

Ƙungiyar ma’aikatan wutar lantarki ta Najeriya (NUEE) reshen Jihar Kano, ta tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani saboda rashin biyan haƙƙoƙinsu da kamfanin KEDCO ke yi.

Sakataren tsare-tsaren ƙungiyar na shiyyar Arewa maso Yamma, Muhammad Babangida ne, ya bayyana hakan a wani saƙon murya da Freedom Radio ta wallafa.

Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”

A cewarsa, ma’aikatan KEDCO sun shafe sama da watanni 100 ana cire musu kuɗin fansho daga albashinsu, amma ba a tura kuɗin zuwa inda ya dace ba.

“Tun bayan kafa KEDCO aka fara cire wa ma’aikata kuɗin fansho, amma har zuwa yanzu ba a tura su inda ya kamata.

“Waɗanda suka mutu ko suka bar aiki suna cikin wannan hali, ba a biya su haƙƙinsu ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa duk wani ƙoƙarin da suka yi don sulhu da kamfanin ya ci tura, hakan ya sa suka yanke shawarar shiga yajin aiki.

Ya ce: “Kamfanin KEDCO yana samun kuɗi sosai, amma ya gaza biyan haƙƙin ma’aikata.

“Saboda haka, daga idan mutane sun ga an samu katsewar wuta, ka da su ɗora laifi a kanmu.”

Yajin aikin zai shafi harkokin samar da wutar lantarki a Kano da kewaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama yarinya kan kashe jariri a sansanin ’yan gudun hijira
  • An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya
  • Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa
  • Mai kwashe sharar da ya shekara 40 yana tara kuɗin Hajji ya isa Saudiyya tare da matarsa
  • Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
  • Madagascar ta kawo karshen cutar shan inna a tsibirin
  • Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano
  • Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
  • Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya